DARAJAR MACE A MUSULUNCI

DARAJAR MACE A MUSULUNCI​

DARAJAR MACE A MUSULUNCI

المرأة في ظلال الإسلام بلغة الهوسا

 

Mawallafi

Dr. Abd Ar-Rahman bin Abd Al-Kareem Ash-Sheha

د. عبد الرحمن بن عبد الكريم الشيحة

 

Fassara

European Islamic Research Center (EIRC)

المركز الأوروبي للدراسات الإسلامية

& Muhammad Khamis

Wanda ya bibiyi fassara

Hashim Muhammad Sani

www.islamland.com

 

 

DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI

GABATARWA

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, tsrira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabin mu Muhammad da iyalan sa da sahabban sa baki daya, bayan haka:

Allah madaukaki yace: " yaku mutane kuji tsoron Allah wanda ya halicce ku daga na miji da mace kuma yasanya ku kuka zama mutane da kabilu domin ku samu sanayya da juna, lallai wanda yafi kowa a cikin ku a wurin Allah shine wanda yafi jin tsoron sa"[1].

            Lallai daga cikin kura kura masu girma da yawa shine a jinginawa musulunci abunda baya cikin sa daga cikin haka akwai fadin da akeyi cewa musulunci baya daraja mace da girmamata sai dai toye mata hakkokinta da yakeyi Allah kuma yana cewa cikin alqur'ani: " idan kuji kyamace su to wata kilafa kina kyamatan abun amma Allah yasa masa alheri me yawa"

(suratun nisa'i ayata 19).

Yana kuma cewa: " daga cikin ayoyin say a halatta maku mataye daga gare ku domin ku samu natsuwa zuwa gare su kuma yasanya tausayi da rahama a tsakanin ku, lallai acikin haka akwai ayoyi ga mutane masu tunani"

(suratul rum ayata 21).

Kuma hakika yawan kira da cewa da cewa aba mace hakkinta da mutuntata da kuma neman daidaita ta dana miji yana kara yawaita kuma hakan ya kamata ne ya kasance cikin al'ummar da suke toye ma mace hakkinta ko kuma kuke hanata hakkin nata amma ba abu bane na hankali ace arika irin wannan kiraye kiraye cikin al'umma musulmai wanda yaba mace hakkokinta da yancinta cikin addini tun gabanin fitowan wannan kiraye kirayen ya kuma sanya wannan hakkoki a matsayin wajibi na shari'a wanda babu makawa akai na hanashi, wannan abu ne me matukar mamaki, hakika ana samun wanda suke muna nawa mace da kuma tuye mata hakkokinta cikin musulmai amma hakan yana faruwa ne saboda rashin riko da karantarwan addinin muslunci da shiryarwan shi me adalci!!.

Lallai masu kira ga a ba mace yancinta da hakkokinta kamar yadda suke ikirari[2] wannan kiraye kirayen nasu yana kaiwa ya komo ne tsakanin abubuwa guda uku:

  1. Neman ba mace yancinta
  2. Daidaita mace dana miji
  3. Neman a bata hakkokinta.

 

Neman ba mace yancinta:

Lalali Kalmar yancin mace yana kunsan cewa akwai wani abu kayyadajje wanda ake nufi, sabod akalmar akwai kusukure acikinta kuma ta kunshi abubuwa da yawa domin zai rika zuwa zuciyar mutum cewa ita baiwa ce tana bukatar a yantata daga bauta, lallai asalin Kalmar yanci abune mawuyaci, mutum yanada iyaka da dabi'ar sa, saboda ikon sa da da iyawar sa kayyadajje ne, mutum a cikin al'ummar sa na birni ne ko na kauye suna rayuwa ne karkashin wani dokoki da tsari wanda suke binsa domin gudanar da rayuwan su da kuma tsara harkokin sun a rayuwa to shikenan hakan yana nufin basu da yanci kenan?! Kenan yancin tanada iyaka wanda idan ka wuce shi sai ka fada matakin dabbobi wanda suke rayuwa ba tare da wani tsari ba kuma basa aiki da dokoki, farfesa Henry Makow yana cewa: (wanda mutum ne me tunani kuma dan makaranta dan amerika kuma me bincike a fannin harkokin mata a duniya)[3] lallai yancin mace da ake kira yaudara ne sabo cikin yaudaran tsarin duniya sabo, yaudara ce tsantsa gwaro wandaya rudi matan amerika kuma ya lallata tsarin turawa.

            Kalmar gaskiya itace cewa musulunci shine farkon addini wanda yaba mace yancin mu'amala kai tsaye da al'ummar ta bayan da mu'amalar ta baya kasance wa sai ta hanyar waliyyinta ko kuma wanda yake rikonta, lallai musulunci be hana mace yanci ba sai yanci na fitsara da rashin kunya me halakarwa irin wannan yanci kuma shima na miji an haramta mashi su dai dai da dai dai, lallai ma'anar yancin a musulunci yana takaita ne cikin fadin mazanon Allah s.a.w: " misalign wanda yake dagewa akan umurnin Allah madaukaki da wanda yake keta su kamar misalign mutane ne wanda sukayi kuri'a a cikin jirgin ruwa sai wasunsu suka cinki saman jirgin wasunsu kuma suka cinki kasan jirgi, sai yakasance idan na kasan jirgin sunajin kishin ruwa sai suje gun nasaman suce masu da ace zan fasa dakan daga cikin kasona na wannan jirgi kuma bazan cutar dana samana ba, idan suka kyale su akan aikata abunda suke so dukansu zasu mutu amma kuma idan suka hana su aikata hakan shikenan zasu tsira daga nitsewa cikin ruwa sai su tsira dukkan su baki daya"[4].

            Wannan shine ma'anar yanci a muslunci ya kasanc cewa harkokin mutum sune tsare da dokokin addini wacce ta kunshi hana cucuwa ga mutum da kuma al'ummar sa.

            Lallai abunda masu kira akan yancin mace suke shine yafi dacewa ko kuma duk wani doka wanda ya dace da maslaha da kuma kiyaye karamar mace da tsare al'umma? Shin tsarin musulunci wanda ya dauki mace a matsayin cikon namiji da abokiyar sa shi yafi ko kuma wannan tsari wanda aka kirkoro daga mutum da dokoki na duniya baki daya wacce akwai abubuwa da dama a bayanta na hadafi da manufa wanda zubar da mutunci ya duma halatta abunda da Allah ya haramta kuma take rusa al'umma da kifar da mulkin kasa?

 

Daidaita mace dana miji:

Lallai neman daidaita mace dana miji cikin dukkanin komai abu ne wanda bazayyiwu ba saboda banbancin dabi'ar kowa daga mace dana miji, ta bangaren jiki ko kuma hankali ko kuma jarumta. Idan daidaito tsakanin jinsi daya watan jinsin na miji da na miji ko kuma jinsin mace da mace abu ne wanda bazayyiwu ba saboda samun banbanci da sabani a tsakanin su abunda yafi dacewa wurin tsananin rashin yu'uwar sa shine idan jinsi yasha banban, Allah madaukaki yace: " kuma a cikin ko wani jinsi na abu mun halitta mace da na miji koda zakuyi tunani"[5].

(Hakan kuma ya faru ne bayan Allah ya halicci jinsi guda biyu sai ya sanya kowa akan yanayin halitta wanda yasha banban da dayan kuma ya zama abokin zaman sa a lokaci guda wanda baya rayuwan sa baya cika sai dashi, idan muka kalli jinsi zamuga cewa ya rabu zuwa nau'i biyu zamu iya cewa be kasu zuwa nau'i biyu ba hakanan face sai dan kowa a cikin su ya kebantu da aikin sa idan bah aka ba da ace aikin daya ne da ya sun kasance jinsi daya ba tare yay a kasu ba zuwa nau'i biyu ba , kena kasuwar su zuwa nau'i biyu dalili ne akan cewa ko wani nau'i yanada nashi siffofin daya ke banta dashi na karon kansa amma kuma jinsi ya hadasu….. daga cikin haka misalign akan haka shine dare da rana nau'i ne biyu na jinsin daya, wannan lokaci na hutawa ne da natsuwa watan dare kenan shi kuma rana lokaci ne na nema da kokari, na miji da mace da irin wannan yanayi, nau'i ne biyu na jinsi daya watan mutum sai ya kasance akwai wasu abubuwa da ake nema daga ko wannen su da siffarsa na mutum , wasu daga cikin wannan abubuwan agun na miji kadai ake neman su wasu kuma agun mace ta yadda zamu iya cewa su nau'i ne biyu na jinsi daya kowa yanada aikin sa wanda yake aikatawa a karkashin kasancewar su jinsi daya sannan kuma akwai aikin da ya shafi ko wani nau'i a cikin su)[6].

Wannan misalin daya gabata zai kara fito mana da rashin yuwawar dai daito tsakanin mace dana miji cikin komai a fili kuma neman hakan zai kasance shiririta ne kokarin neman aikata hakan saboda ya kasance kokari ne akan canza fidirar da dabi'a koma alokaci guda kokari ne na neman wulakanta mace da kaskantar da ita wanda hakan zai sanyata canzawa daga dabi'arta wanda Allah ya halicce ta akai wanda hakan zai harfai da sakamako mummuna ga al'umma.

 

Neman ba mace hakkokinta:

Babu wani doka ko kuma tsari tsoho ko kuma a wannan zamani namu wanda ya kiyaye hakkokin mace ya kuma daga darajarta kamar yadda musulunci ya kiyaye mata, tun lokacin da hasken musulunci ya bayya ta hanyar aiko da manzon Allah Muhammad s.a.w wacce ta dasa wani canji cikin zukatar musulmai wanda sukayi imani dashi kuma ta sanadiyyar su ne cikin zamantake wa ta al'umma dan adam aka samu canji sabo cikin tarihin mutum, labarin ya kasance sabo cikin komai cikin saurin yaduwar sa da karade komai dayayi da kuma saukin sa ga fahimta da dacewa da fidirar mutum, bubu wani duhu a cikin sa ko kuma rufa rufa ko cin karo da fidirar mutum melafiya a cikin sa, bari mu dauka daga cikin wannan labari cikin abubuwan daya zo dashi na canje canjen kallon da akeyi ma mace a baya zuwa canza darajar mace da hakkokinta wanda wannan shine maud'in mu na wannan rubutu, me littafin wayewar larabawa yana cewa[7]: falalar musulunci be takaita ba kawai akan daga darajar mace ba kawai zamu kara akan haka cewa shine farkon addini wanda ya aikata haka.

Ya kuma kara fadi a wani wuri cikin littafin a shafi na 497: hakkokin ma'aurata wanda qur'ani ya nassanta hakan da kuma masu fassara shi yafi falala dayawa akan hakkokin ma'aurata na turawa.

Lallai hakkokin mace ya kamata a neme shi a wurin al'ummar da suka kwace masu hakkokin su cikin zamanta kewar su ko kuma suka basu hakkoki mara tsari wacce take sanya mace fadawa a karkashin su cikin dabi'u masara kyau da fasadi ta kuma koma kayar wasa da biyan bukata da jin dadi, amma a musulunci lallai yayi ma mace adalci.. kuma yak are mata hakkokinta ya kuma bata hakkokinta na gabaki daya da na musamman wacce zata iya rayuwa ta hanyar su rayuwa me kyau da aminci kuma tayi ayyukan da Allah ya halicce ta domin su.

 

 

 

YANAYIN MACE CIKIN ZAMUNAN DA SUKA WUCE DABAN DABAN

HALIN MACE CIKIN AL'UMMAR JAHILIYYA:

Hakika mace ta kasance cikin al'ummar jahiliyya kafin zuwar musulunci abun garkuwa da tsoro da kuma zalumci, ana cinye hakkokinta da kuma kwace mata dukiyarta kuma ana daukar ta a matsayin kayan jin dadi ne kawai wacce bata da wani kima ba'a bata gado saboda gado ba'a bayar dashi sai ga wanda zai iya hawa kan doki ya fita filin yaki ya fafata ya samo ganima hasalima ita mace gadonta akeci idan mijinta ya rasu kamar yadda ake gadon sauran kayayya, idan mijinta yanada yara wand aba yaranta ba kuma ya zama shine yaronshi na farko to shine yafi cancanta da matar babanshi akan wanin sa zaici gadonta kamar yadda ake gadon dukiya kuma bazata fita daga gidan sa har sai ta fanshi kanta, kuma ana hanata koma wurin mijinta bayan ya saketa kuma na miji zai iya auro mata adadin matar da yakeso ba tare da wani kayyadewa ba kuma bata da hakkin zaban mijin da takeso kuma bata da wani hakkoki akan mijinta kuma babu wani doka wanda zai hana mijinta zalumtar ta, labarawa sun kasance a zamanin jahiliyya basa maraba da haihuwan yara mata bassoon haka suna masu daukan haka a matsayin babban sharri da bala'i, idan kuma aka haifan ma mutum yarinya mace sai damuwa da bakin ciki ya kamashi, kuma hakika kin matan da sukeyi yakai matakin kisa, kisan yara mata ya kasance yana faruwa agun wasu kabilun larabawa kuma dalilan haka suna banbanta sabanin yanayin iyalai cikin al'umma, daga cikin su akwai wanda suke kashe yara mata saboda tsoron abun kunya, daga cikin su kuma akwai wanda suka kashe yara mata idan ta kasance tanada wani aibu na halitta kamar rashin lafiya, Allah madaukaki yace yana me wasifta halinsu cikin wannan al'amari: " idan kuma akayima dayan su bisharar samun yarinya mace sai kaga fuskarsa ta canza yana cikin fushi da bacin rai (58) yana buyema mutane saboda abun munin abunda aka masa bishara dashi kodai ya rike ta cikin wutakanci ko kuma ya birne kasa ya rufeta da ranta, ku saurara kuji abunda suke hukuntawa ya munana"[8].

Daga cikin su kuma akwai wanda yake kashe yaransa mata saboda tsoron talauci watan talakawa cikin larabawa, kuma hakika alqur'ani ya rubuta hakan cikin fadin Allah madaukaki: " kada ku kashe rayan ku domin tsoron talauci lallai mune muke azurta su da ku baki daya, lallai kashe su ya kasance kuskure ne babba"[9]

Mace ta kasance bata more hakkokinta na dabi'a daga cikin abinci ma akwai wanda na maza ne kawai haramun ne ga mata, Allah madaukaki yace: " kuma sunce abunda cikin wannan dabbobi na cin mazajen mu ne kawai haramun ne ga matan mu"[10].

Bata da wani abu wanda zata rika alfari dashi inba kariyan namiji ba akanta da kuma daukan mata fansa idan an keta mata darajarta da kuma kiyaye martabanta.

 

HALIN MACE CIKIN AL'UMMAR HINDU NA FARKO:

Yazo cikin littafin (FIDYA) daya daga cikin littafi me girma wanda yake ya kunshi tushen addini a cikinsa na barahimiyya cikin abunda ya shafi mace cewa[11]: shari'ar barahimiyya ya banbanta tsakanin namiji da mace cikin darajar mutum da sauran hakkoki, ya kwace ma mace dukkanin wani matsayi nata na rayuwa yasanya ta karkashin ikon namiji cikin dayawa daga cikin matakai na rayuwanta kamar yadda dokokin su na manu ya nassa haka kamar yadda ya hukunta cewa beya halatta ga mace cikin cikin matakai na rayuwanta ta gudanar da wani abu karkashin ganin damarta koda kuwa wannan abun na harkokin cikin gidanta ne, a lokacin yarantanta kuwa tana bin ubanta ne, a matakin budurcinta kuwa taka karkashin mijinta ne, idan mijin nata na yutu sai jagorancinta ya goggonta, idan kuma bata da goggo sai wannan jagorancin nata ya koma zuwa ga shugaba, mace dai bata da wani yanci na rayuwanta cikin dukkanin matakai na rayuwarta na cin gashin kanta na gudanar da ayyukanta yadda take so.

Halin mace ya kasance cikin al'ummar hindi kamar halin matan aure wacce take karkashin mijnta bata da wani iko cikin al'amrinta da komai hasali ma zai iya a asaranta a wayan caca da sukeyi[12].

Bazatayi aure ba bayan mutuwar mijinta batada wani hakki na rayuwa bayan mutuwar sa hasali ma dolene ta mutu itama ranan da mijinta yam utu a konasu a wuri daya, wata marubuciyar su na addini tana cewa[13]: anaso ga matan da mijinta ya mutu da taje fa kanta cikin makashin wutan da aka hada domin kona mijinta wanda yam utu, sun kasanc eidan sun sanya gawar acikin wannan makamashi na katakai sai matan tazo fuskarta a rufe sai bokan su me suna barahima yazo ya dagata ya cire mata kayanta na ado a rabama yan uwanta sa'annan babban wannan bokaye ya kama hannunta na dama su zagaye wannan makamashi sau uku sa'annan a dauarta akan wannan katako sai ta daga mijin zuwa goshinta alamar jirmamawa gareshi sai daganan ta zauna ta wurin gansa ta daura hannunta na dama akanshi sai a zo da wuta a konasu tare, suna kudurce hakan zai gadar mata da ni'ima tare da mijinta zasu zauna tare a sama shekaru miliyan talatin da biyar… sannan kuma wannan konata din da akayi zai tsarkake iyalanta na bangaren mahaifiya dana bangaren mahaifi da iyalan mijinta da kuma tsarkake mijinta daga dukkanin zunuban sa… sannan kuma tana cikin mata masu tsarki da daraja acikin su wurin suna kuma me kyakyawan sauti, wannan al'adar ta yadu a tsakanin su yaduwa me girma yadda suka kona sama da mata dubu shida cikin shekaru goma kacal daga shekara ta 1815a.d zuwa shekara ta 1825a.d kuma anci gaba da amfani da wannan shari'a har zuwa karshen karni na goma sha bakwai wanda daganan ne akayi watsi da wannan al'ada abisa tilastawa na malaman addinin hindu.

Daga cikin abunda yake nuni akan halin na kunci wanda mace take rayuwa a cikinta cikin addinin hindiyya a wannan lokaci shine abunda yazo cikin dokikin addinin hindus yadda take cewa[14]: kabari da iska da mutuwa da jahannama da guba da annoba da wuta basufi mace muni ba.

Mace ta kasance cikin wasu lokuta tanada mazaje da yawa halinta kamar halin karuwa dai dai bawani banbanci.[15]

 

HALIN MACE CIKIN AL'UMMAR KASAR CHINA NA FARKO FARKO:

Mace ta kasance cikin al'ummar china na farko farko kmaar yadda me littafin kissar wayewa[16] ya kawo: mace tana karkashin najimi ne tana kare rayuwanta ne karkashin biyayyar sa kamar kuma yadda aka haramta mata dukkanin hakkokinta na dukiya dana zamantakewa ta kasance mara iko wacce bata mallakar komai cikin al'amuranta hasali ma na miji shine magajinta acikin haka baki daya, kamar kuma yadda bata da yancin yin karatu ko kuma samun wata wayewa dole ne ta zauna cikin gida a killace tana aiki da koyan dinki da sauran ayyuka daban daban, kuma dole ne akanta da ta aske gashin kanta idan takai shekaru goma sha biyar kuma dole ne tayi aure idan takai shekaru ashirin sannan kuma mahaifinta shine wanda zai zaba mata miji tare da taimakon dillalai.

Sannan haihuwar mace yana matsanin babban zunubi ne, W.Durant yana cewa cikin littfain san a kissar wayewa[17]: lallai iyaye sun kasance suna addu'a cikin sallolin su da a azurta su da yara maza kuma ya kasance cikin manyan dalilai na wulakanta mata koda yaushe shine ya zama cewa basu da yara maza, saboda yara maza sunyi karfin yin aiki sama da yara mata da kuma karfin zuciya da jarumtaka a fagen yaki, yara mata sun kasance suna daukar su amatsayin kaya ga iyayen su saboda suna renon su da kuma hakuri akan tarbiyyar su daganan kuma su kaisu gidajen mazajen su.. hatta al'adar kashe mata akwai shi a lokacin ta yadda idan aka haifan ma iyali yara mata dayawa sama da bukatuwar su kuma wannan iyali ta gagara ko kuma sha wahala wurin ciyar dasu sais u barsu cikin daji domin hankaka ya cinye su cikin dare ko kuma namomin daji masu cutarwa ba tare da mutanen wannan iyali ba sun san wani abu cikin wannan aiki mummuna.

Wani daga cikin jagorori na china a wannan lokaci ya kasance yana cewa[18]: ki saurari mujinki kuma kada ku gasgatata.

 

HALIN MACE IKIN AL'UMMAR ROMAWA NA FARKO FARKO:

Me littafin kissar wayewa yana cewa:[19] haihuwar mata ya kasance abune wanda ake kyama hasalima al'ada ta halattama iyaye idan an Haifa masu yara masu illa ko kuma mata su kashe su sannan kuma sabanin haka sun kasance suna son a haifan masu yara maza.

Hakika mace ta kasance cikin al'ummar rumawa mara yanci wacce taba mallakan komai cikin al'amarinta na miji shine wanda yake tafiyar da ita yadda yake so cikin komai sannan kuma iko yana hannun namiji ne shi kadai ya kasance yana da hakkoki sjhi kadai cikin dukkanin mutanen gidansa ya kasance cikin ikon nasa yana da daman hukunta kisa ga matar shi a halin tuhuma [20] kuma yanada iko akan matan yaran sa da jikokin sa, sannan kuma wannan iko ya kunshi siyarwa da azabtarwa da korar mutum da kuma kisa.

Aikin mace shine ji da biyayya da aiwatarwa amma bata da wani iko na kalubalanta ko kuma neman gadonta wanda aka haramta mata saboda gado babban yaro namiji kawai ake dankamawa al'amarin ya cuwe nan yakai da cewa mutum namiji yanada hakki shiga iyalin da banashi ba kuma ya fitar da wanda yakeso acikin yaran ta hanyar siyarwa.[21]

 

HALIN MACE CIKIN AL'UMMAR JAMUSAWA NA FARKO FARKO:

Mace bata da wani rabo cikin al'ummar zamusawa bare kuma rabo cikin mutanen da suka gabata, wulakantarwa ga mata yakai da cewa ana iya bayar dasu rance, TARWILUNG yana cewa[22]: mace me haihuwa ta kasance ana daukan hayanta daga mijinta domin da haifama kasa yara maza daga wani miji na daban.

Kuma an haramta mata wani wayewa wanda yakai darajar an ayyanata da cewa (mace datti ne daga cikin aikin sheda)[23].

Babu wnai tsari wanda zai kareta daga haramcin samun gado bata da yanci na amfani da dukiyarta, an kwace mata dukkanin yanci da zabi rayuwanta yana gudana ne karkashi ikon namiji bata da wani hakki na neman saki saboda wannan hakki ne kai tsaye na namiji[24].

Al'amarin a wurin su ya kai matsayin wasu daga cikin masu tunanin su suna kira da a rika kulle sunan mata cikin gida kamar yadda ake rufe gangar jikinta.[25]

Mace bata kasance ba cikin al'ummar jamusawa face halitta wulakan tacciya wacce take can kasa, me littafin wayewar labarawa yana cewa[26]: " al'agrik ya kasance yana irga mata cikin halittun da basu da wani amfani wanda ya wuce dawwamar zuriya da kuma tafiyar da gida, idan mace ta haifi yaro mummuna kuma sai ya zaman mata kaya.

Me Magana da yawunsu shahararre ya sawwara halin mace da cewar sa[27]: mu muna rike mata karuwai ne a matsayin abun jin dadi, da mata kawaye domin kula da lafiyar jikin mu, su kuma matan mu muna auran su ne domin su haifan mana yara a shari'ance.

Ina rabon mace yake cikin wannan al'ummar da masu ilimin su suka fadi wannan Magana?!

 

HALIN MACE CIKIN AL'UMMAR YAHUDAWA NA FARKO FARKO:

Mace a wurin yahudawa asalin zunubi ce kuma asalinta kamar yadda yazo cikin attaura[28]: mace itace mafarin zunubi kuma itace sanadiyyar batan mutane baki daya.

Halon mace cikin al'ummar yahudawa babu dadi kuma sun rubuta dokoki akanta da tsawatarwa daga gareta kamar yadda suka wasafta cikin (safar aljami'ah)[29]: na tarbiyyantar da kaina domin sani da rayuwa da kuma neman hikima da hankali da kuma sanin sharrin jahilci da asalin hauka sai na samu cewa al'amari na mutuwar mace wacce itace wundoji sannan kuma zuciyarta sharri ne hannunta kuma shine sharadi a gaban Allah babu wanda zai tsira daga gareta sai me kuskure wanda za'a kamashi da laifinta.

Baba yanada iko na kai tsaye cikin iyalan sa musammam ma mata zai aurar dasu ga wanda yake so ko kuma ya bada su kyauta ga wanda yakeso sannan kuma zai iya siyar dasu idan yaso kamar yadda yazo cikin littafin safar alkhuruj alishah na ashirin da daya cikin sakin layi na 7 zuwa 11.

Me littafin kissar wayewa yana cewa[30]: baba yana da wani irin karfin iko cikin iyalansa wanda bata misiltuwa kasar ya kasance nashi ne sannan kuma rayuwan yaransa ya alaka ne da biyayyar da suke masa, ya kasance daula kacokan sannan yana cikin ikonsa idan ya kasance talaka ya siyar da yarinyar sa kafin ta balaga domin ta zama baiwa kamar yadda har wayau yake da hakki na aurar da ita ga wanda yakeso dukda a wasu lokutan ana samu nayan iya janyewa daga wannan hakki nasa ya bata daman yarda da wannan miji.

Idan mace bayahudiya tayi aure ikonta ya tashi daga kan babanta zuwa ga mijinta ta zama daya daga cikin kayansa wanda ya mallaka kamar gida da bawa da baiwa da dukiya, wannan shine abunda hukunce hukuncen attaura ya nuna akai cikin littafin safar alkhuruj alishah na ashirin, sakin layi na:17.

Kari akan haka shine shari'ar yahudawa ya haramtawa mace gadon babanta idan yanada yara maza kamar yadda yazo cikin safar al'adad alishah na ashirin da bakwai, sakin layi na: 8: duk mutumin da ya mutu bashi da yaro na miji dukiyar sa zai koma zuwa ga yarinyar sa mace.

Matar aure a wurin su daga lokacin da mijinta ya mutu zata koma karkashin dan uwan mijinta ta yarda ko bata yarda ba sai dai idan yace bayaso kamar yadda yazo cikin littafin me girma tsohon alkawari[31]: idan yan uwa biyu suna zaune sai daya daga cikin su ya mutu kuma bashi da yaro na miji wannan matar tashi bazata koma gidan wani mutum a waje ba, dan uwan mijinta sai shiga ya dauke ta a matsayin mata a gareshi ya ci gaba da daikan dawainiyar mijinta dan uwanshi da ya mutu akanta.

Kuma sun kasance basa cin abinci da shan ruwa da kwana da mace me al'ada suna nesantar ta har sai tay tsarki, dokar su yana cewa cikin wannan al'amari[32]: lallai mace bata da tsarki tun daga narar da tafara jin alamun al'adarta na wata wata koda kuwa babu wani alama na fili akan haka sannan kuma haramun ne ga mijinta ya tabata koda kuwa da yatsansa ne karamin kuma ba'a yardan masa ba da yabata wani abu koda kuwa daga nesa ne ko kuma ya amshi wani abu daga gareta, sannan kuma jefa mata abubuwa daga hannunsa shima ba'ayardan masa ba, sannan ba'a yarda daya ci abinci tare da itaba a kwano daya sai dai idan wani abu ya raba tsakanin su, haka kuma ba'a yardan masa ba da shan sauran ruwan da ta rage cikin kofi ba ko kuma kwana a gado daya ko hawan mota daya ko daya ya kusanci daya ba idan kuma sun kasance a wurin aiki daya to da sharadin bazai tabata ba, sannan idan mijinta bashi da lafiya kuma babu wanda zai tsaya masa sai ita to hakan an yardan mata matukar bazat tabashi b aba tare da wani tsamaki ba amma idan matar ce bata da lafiya to ba'a yardan ma mijin ba da ya tsaya mata koda kuwa bazai tabata ba, sannan macen da ta haifi yaro daga ta tsahi a matsayin mara tsarki, idan namiji ta Haifa zata zauna tsawon kwanaki bakwai a haka, idan kuma macece ta Haifa zata zauna tsawon kwanaki goma sha hudu a matsayin mara tsarki sannan bazatayi wanka ba sai bayan kwanki arba'in daga haihuwar na miji ko kuma kwanaki tamanin idan mace ta Haifa.

 

HALIN MACE CIKIN AL'UMMAR KIRISTOCI NA FARKO FARKO:

Iyayen coci na zamanin tsakaya suna daukan mace a matsayin itace asali na zunubai da sabo da kuma dalilai na musifa wanda suka samu mutum, saboda haka ne alakar namiji da mace ya zama datti wanda ya zama wajibi ya nisanta daga gareshi koda kuma ta hanyar aure ne na shari'a babban malamin su Tartoliyan yana cewa: mace hanyar shedan ne zuwa ga zuciyar mutum kuma tana jan mutum zuwa ga mishiyar tsinuwa wanda yake warware dokokin Allah na namus wacce take dadashe surar Allah -watan mutum namiji-.

Kuma mawallafi Donw mirky Wieth Knudesen ya bayyana darajar mace cikin mazanin tsakiya da cewa: damuwa da mace ya kasance dan kadan saboda bin mazhabar katolikan wacce yake daukan mace a matsayin wacce aka halicce ta cikin martaba ta biyu.[33]

Bulus manzo yana cewa[34]: inaso ku sani cewa lallai shugaban ko wani namiji shine almasihi amma shugaban ko wace mace shine namiji kuma shugaban almasihi shine Allah…lallai baya halatta ga namiji daya rufe asalinsa saboda kasancewar sa suran Allah da mujaddadin sa, ita kuma mace mujaddadin namiji ne saboda namiji ba daga mace yake ba ita macence take daga namiji kuma saboda namiji ba'a halicce sa ba domin mace ita macence aka halicce ta domin na miji saboda haka ya zama wajibi mace ta kasance tana da shugaba a samanta saboda mala'iku.

Hakika karantarwan almasihi yana wajabtawa mace kasancewa me biyayya a karkashin namiji kuma biyyar namiji kamar biyayya ne ga malamai, bulus yana cewa[35]: yaku mata kuyi biyayya ga mazajen ku da kankantar da kanku garesu kamar yadda zakuyima ubangiji saboda namiji shine shugaban mace kamar yadda almashi shine sugaban cuci.

Barnard shoe malamin adabi na turanci yana cewa: daga lokacin da mace ta aure namiji dukkanin abubuwa mallakinta zai koma na mijinta karkashin dokokin turawa.

Wannan kari ne ga wanzuwar aure har Abadan wanda addini ya wajabta da dokoki, duk inda gaba da kiyayya yakai tsakanin ma'aurata da kuma girmaman matsaloli a tsakanin su babu maganar saki sadai hakan zai koma zuwa ga rabuwan jiki wanda daga cikin dabi'ar haka shine na miji ya samu kawa mace da abokai mata itama matar da samo abokai maza wanda zasu rika zama tare.

Kamar yadda idan daya daga cikin ma'aurata ya mutu to dayan bashi da damar karayin wani auren kuma, sai yazama sakamakon haka ya toye darajar mace ya kuma toshe ikonta wanda hakan yakai haifar da munanan dabi'u cikin al'ummar turawa na wannan zamani ta yadda masu tunanin su da masu wayewar su sukayi kiran aba kowa ciki mutanen al'umma namiji ne ko mace yancin sa da hakkokin sa mara iyaka wanda hakan ya haifar da alkibla mummuna wanda sakamakon hakan shine abunda wannan al'aummar take rayuwa akai a yau na rashin dabi'u da daidaita iyalai dukkanin haka sakamakon coci ne da dokokinta na zalumci wanda yaci karo da fidirar me hankali.

 

 

HAKKOKIN MACE A CIKIN MUSULUNCI

bayan wannan dubi na gaggawa da muka kawo na halin mace cikin al'ummomi gabanin zuwan musulunci bari muga darajar mace da hakkokinta wanda musulunci ya bata, mata suna da hakkoki cikin musulunci wanda sukayi tarayya da kowa aciki da kuma wanda suka kebanta dashi su kadai, daga cikin hakkokin mace wacce tayi tarayya dashi da sauran mutane cikin musulunci shine:

  • Mace dai dai take da namiji wurin ibada da ayyukan da Allah ya wajabta cikin hukunce hukuncen shari'a ta yadda ya wajabta mata abunda ya wajabtawa namiji idan sharuddan talafifanci ya cika akanta wanda sune (muslunci- balaga- hankali) na salla da zakka da azumi da hajji sai dai Allah ya kebance mace ta hanyar sawwaka masu wasu daga cikin ayyukan shari'a kamar dauke mata salla da azumi a lokacin al'adarta da lokacin jinin haihuwarta sannan zata rama azumi ne kadai bayan tayi tsarki saboda lura da yanayinta na jiki da ranta a lokacin al'ada da jinin haihuwa.
  • Mace kamar namiji ne wurin lada da azabtarwa dunuya da lahira, Allah madaukaki yace: " duk wanda ya aikata ayyuka na kwarai cikin maza da mata yana kuma mumini to hakaki zamu yarashi rayuwa me kyau, kuma zamu saka masu da lada wanda yafi abunda suka aikata (97)"[36].
  • Mace kamar namiji take ta fuskar halitta ba ita bace asalin zunubi kuma ba ita bace dalilin fitan annabi adam daga aljanna ba kuma ita ba jinsi bace mafi kaskanci kamar yadda malaman addinin da suka gabace mu suke fadi, Allah madaukaki yace: " yaku mutane kuji tsoron ubangijin ku wanda ya halicce ku daga mutum daya ya kuma halitta masa mata daga jikinsa ya kuma yada maza da mata dayawa daga garesu, kuji tsoron Allah wanda kuke roka buqatunku kuma kuke sada zuminci domin sa, lallai Allah ya kasance me sanya ido akanku (1)"[37]

Allah madaukaki ya bayyana cikin wannan aya cewa ya halicci jnsin namiji da mace daga asali daya babu banbanci ta bangaren asalin halitta a tsakanin su ko kuma cancanta dukkansu daya suke, da wannan aikin ne musulunci yayi watsi da abunda ya yadu na dokokin zulumci ga mace wanda yake daukan mace a matsayin me dabi'a wanda bekai na namiji daraja ba wanda hakan yake haifar da hanata dayawa daga cikin hakkokinta na dan adam, manzon Allah s.a.w yana cewa: " lallai mata shakikai ne ga maza"[38].

  • Mace daidai take da namiji wurin wajabcin kiyaye mata mutumcin ta ya tsare mata karamarta, musulunci ya sanya ukuba akan yima mace kazafi da kuma keta mutuncinta, Allah madaukaki yace: " wanda suke jifan mata kamulallu masu aure da aikata zina sa'annan kuma basu zo da shaidu ba to kuyi masu bulala tamanin kuma kada ku amshi sheda awurinsu har Abadan kuma wannan sune fasikai (4)"[39].
  • Mace daidai take na namiji cikin hakkin gado kamar yadda namiji yake da hakkin cin gado, Allah madaukaki yace: " maza suna da rabo cikin abunda mahaifa biyu suka bari da yan uwa haka suma mata suna da rabo cikin abunda mahaifa biyu suka bari da yan uwa, kadan ne ko dayawa, rabo ne wanda take dole (7)"[40].

Sai musulunci ya tabbatar mata da hakkinta nagado bayan a lokacin jahiliyya ana hanata, hasalima itama gadonta akeyi kamar yadda ake gadon sauran kaya, Allah madaukaki yace:' yaku wanda sukayi imani baya halatta a gareku da ku gaji mata da karfi, kuma kada ku hanasu tafiya da da abunda kuka basu"[41].

Umar dan kaddab Allah ya kara masa yarda yace: ..wallahi mun kasance cikin jahiliyya bama ba mace komai har zuwa lokacin da Allah ya saukar da ayoyi akansu ya kuma basu abunda ya basu…[42]

  • Mace dai dai take dana miji wurin cancanta da kuma yanci na jujjaya dukiyanta na siya da siyarwa da abunda suka kamanci haka na jujjuya dukiya ba tare da an kayyadeta ba cikin jujjuya dukiyanta sai dai cikin abunda akwai cutarwa a gareta kuma ya sabama shari'a, Allah madaukaki yace: " yaku wanda sukayi imani ku ciyar daga cikin dadadan abunka kuke dashi"[43]

Allah madaukaki kuma yana cewa: " lallai musulmai maza da musulmai mata da muminai maza da muminai mata da masu wayan ibada maza da masu yawan ibada mata da masu gaskiya maza da masu gaskiya mata da masu hakuri maza da masu hakuri mata da masu tsoron Allah maza da masu tsoron Allah mata da masu sadaka maza da masu sadaka mata da masu azumi maza da masu azumi mata da masu kiyaye farjin su maza da masu kiyaye farjin su mata da masu ambaton Allah dayawa maza da mata masu ambaton Allah dayawa Allah ya tanadar masu da wata irin gafara da kuma lada me girma (35)"[44]

  • Musulumci ya irga girmama mata daga cikin alamar mutum me hankali cikakke me alheri, manzon Allah s.a.w yace: " wanda yafi muminai cikon imani shine wanda yafi su kyawaun halaye kuma mafificinku shine mafifici a wurin matansa"[45]
  • Ya wahabtama mace karatu da karantarwa kamar yadda ya wajabtama namiji, manzon Allah s.a.w yace: " neman ilimi wajibi ne ga dukkanin musulmi"[46]

Kuma malamai sunyi ittifaki akan Kalmar musulmi anan wurin ya hada da namiji da mace.

  • Mace dai dai take da namiji wurin tarbiyya kowanne daga cikinsu yanada hakkin abashi tarbiyya me kyau akuma reni ne reno na kwarai hasalima musulumci ya dauki tarbiyyan mata da ciyar dasu daga cikin sababin shiga aljanna wannan yana daga cikin abubuwan da mata suka fi maza dashi, manzon Allah s.a.w yace: " duk wanda yake da yara mata uku yayi hakuri dasu ya ciyar dasu da shayarwa da tufatar dasu daga cikin kudinsa da yake sumu daga gumin sa, zasu kasance masa karaya daga wuta ranan alkiyama"[47].
  • Mace daidai take da namiji wurin daukan nauyin gyara al'umma na aiki da kyakyawan aiki dayin hani daga mummunan aiki, Allah madaukaki yace: " muminai maza da muminai mata sashin su yan uwan sashi ne suna umurtan juna da kyakyawan aiki kuma suna hani daga mummunan aiki suna tsaida salla kuma suna bada zakka sannan kuma suna yima Allah biyayya da manzon sa, wa'innan sune wanda Allah zai masu rahama, lallai Allah ya kasance mabuwayi me hikima"[48]
  • Mace daidai take da namiji wurin bada mafaka na amincin, Allah madaukaki yana cewa: " idan wani daga cikin mushrikai ya nemi ka bashi mafaka to ka bashi mafakar har sai yaji maganar Allah sannan kuma ka kiyaye masa alkawarin sa har zuwa lokacin da kukayi dashi"[49]

Kuma manzon Allah s.a.w yana cewa: "…. Zimmar musulmi guda daya wanda yake ba wani kafiri komai kankantan wannan musulmi daya yake da zimmar da kowa zai bayar cikin musulmai, duk wanda ya karya alkawarin wani musulmi to tsinuwar Allah ya tabbata akansa da mala'iku da mutane baki daya kuma baza'a karbo wani aiki ba daga gareshi…."[50]

Wannan wajibi ana kan kowa maza da mat, saboda hadisin Ummu hani diyar abi dalib tana cewa: na tafi wurin manzon Allah s.a.w a shekarar da akaci garin makka da yaki sai na same shi yana wanka dayar sa fadima kuma tana rufeshi sai tace: sai nace masa sallama sai yace: " wacece?" sai nace: nice ummu hani diyar abi dalib sai yace: " maraba da zuwa ummu hani" bayan y agama wankan sai ya tashi yayi salla raka'a takwas yana sanye cikin riga daya, bayan ya gama sallar sai nace masa ya manzon Allah: yaron yar uwata yana yana tsammanin ya kashe wani mutum wanda wane dan hubaira ya bashi mafaka sai manzon Allah s.a.w yace: " hakika mun bada mafaka ga mutumin da kika ba mafaka ya ummu hani" sai tace: a lokacin kuw a lokacin walaha ne[51].

Saboda sanin darajar ta a musulunci mace tana bayar da mafaka cikin musulmai, an karbo hadisi daga abi huraira Allah ya kara masa daga manzon Allah s.a.w yace: " lallai mace tana bada mafaka cikin musulmai".[52] Watan zata iya ba wani cikin kafirai mafaka na zama cikin musulmai. Duk da cewa akwai wasu abubuwa da suka kebanta ga maza kawai banta mata musulumci be daidaita mace da namiji ba acikin su, zamu koro maka sui dan munzo Magana akan shubuhohin da aka kirkiro akan mace.

Kuma ya dace musan halin mace da matsayinta kafin zuwan musulunci da kuma yanayin da suka wayi gari bayan zuwan musulunci a ciki domin dajarar mace me kima ya bayyanar maka cikin musulumci.

Su kuma hakkokin da suka kebanta ga mata kawai hakika musulunci yana kallon mace da idon kima wanda yake yake kira zuwa ga mutuntata da bata hakkokinta cikin dukkanin matakai na rayuwanta tun daga haihuwanta har zuwa mutuwar ta bawai ga mataki daya bane kawai wannan ya takaita, musulumci ya himmatu da ita tana yarinya sannan kuma ya himmatu da ita a matsayin mata ya kuma himmatu da ita a matsayin mahaifiya sannan kuma ya himmatu da ita a karshe kamar mace cikin matan musulmai kuma zamu kawo hakkokinta a dunkule da kuma takaitawa saboda gudun kada mu tsawaita wanda kuma yake son Karin sani akan wanda muka kawo zai iya komawa cikin littattafan fiqhu wanda sukayi bayani dalla dalla akan haka.

 

 

Hakkoki cikin musulunci tana yarinya karama

Hakkinta na rayuwa:

Allah madaukaki ya wajabta akan iyaye da kula da kariya akan rayuwan yaran su maza ne ko kuma mata ya sanya kashe su cikin manyan laifuka, Allah madaukaki yace: " kada ku kashe yaranku domin tsoron talauci mune muke azurta su daku lallai kashe su laifi ne babba"[53]

 Ya sanya ciyar dasu mazan su da matan su hakki ne na wajibi wanda nake lamuntacce akan su akan mahaifin su tun lokacin da suke jariarai acikin mahaifiyar su, Allah madaukaki yace: " idan sun kasance masu ciki to ku ciyar dasu har sai sun haihu"[54].

Hakki nace na shayarwa:

Hakika Allah madaukaki ya wajabta kyautatawa yara maza ne ko mata da himmatuwa da harkokin su da kuma tsayawa da dagewa wurin renon su da biyan bukatunsu na rayuwa kuma musulunci ya sanya haka a matsayin hakki ne na yara akan mahaifinsu, Allah madaukaki yace: " iyaye mata suna shayar da yaransu shekara biyu cikakke ga wanda yake son ya cika shayarwan sa, shi kuma mahaifin akansa ciyar dasu da tufartar yasu yake gwargwadon halin sa"[55].

Hakkin mace na reno da tarbiyya:

Hakika Allah ya wajabtawa iyaye dagewa akan tarbiyyan yaran su maza da mata, tarbiyya ta jiki da ta hankali da kuma na shari'a, manzon Allah s.w.a yana cewa: " ya isa mutum zunubi ya tozarta da wanda yake ciyarwa"[56]

Ya kuma kara fadi yace s.a.w: " dukkan ku mikewata ne kuma za'a tambaye ku akan kiwon da aka baku, shugaba me kiwo ne kuma za'a tambaye shi akan abun kiwonsa, mutum me kiwo ne akan iyalan sa kuma za'a tambayeshi akan kiwon sa, mace ma me kiwo ce akan gidan mijinta kuma za'a tambayeta akan kiwonta, me aiki me kiwo ne akan dukiyar me gidar sa kuma za'a tambaye sa game da kiwon sa"[57].

Kamar yadda zaban masu sunaye masu dadi me ma'ana ya zama dole akan uba, mahaifiya ita tafi cancanta da renon yara akan uba idan an samu sabani a tsakanin ma'aurata aka rabu, hakika musulunci mace yaba hakkin renon yara ba namiji ba saboda shakuwar su da tausayin su kamar yadda yazo cikin hadisin Amru dan shu'aibu cewa wata mata tace: ya manzon Allah wannan yaron nawa cikina ya kasance runbun sa nona na kuma shine abincin sa kuma daki na nan ne mafakar sa, babansa ya sake ni kuma yanason ya kwace shi daga gareni sai manzon Allah s.a.w yace: " ke kika fi cancanta dashi matukar bakiyi aure ba"[58].

Hakkin mace na tausayi da rahama da mu'amala me sauki:

Lallai sunada bukutan wannan kamar yadda suke da bukatar ci da sha domin hakan yana da tasiri sosai akan halayen su da rayukansu shi kuma musulunci addini ne na rahama da jin kai da tausayi da taimakon na nesa to yaya kake gani ga na kusa, an karbo hadisi daga abi huraira Allah ya kara masa yarda yace: manzon Allah s.a.w ya sunbaci Hassan dan Aliyu a wurin akwai Aqra'a dan habis altimimi yana zaune sai yace: inada yara goma amma ban taba sunbatan ko day aba daga cikin su!!! Sai manzon Allah s.a.w ya kale shi yace masa: " duk wanda baya tausayi baya tare damu"[59]

Hakkin mace na karatu:

Musulunci ya sanya neman ilimi wajibi ga ko wani musulmi, manzon Allah s.a.w yana cewa: " neman ilimi wajibi ne akan ko wani musulmi"[60].

Ya sanya karantar da mata karon kansa cikin dalilai na nunka lada, manzon Allah s.a.w yana cewa: " babu wani mutum da zai kasance akwai yarinya karama a wurinsa na baiwa sai ya karantar da ida ya kuma kyautata karantarwan tata ya kuma tarbiyyantar da ita ya kuma kyautata hakan sa'annan kuma ya yantata ya kuma aure ta to yana da lada biyu"[61].

Hakkinta na daidaito:

Musulunci ya wajabta daidaito da adalci tsakanin yara a takaice babu banbanci wurin mu'amalantar su da rahama da tausayin iyaye akan yaransu maza da mata saboda fadin Allah madaukaki: " lallai Allah yana umurni da adalci da kyautatawa da bayar da sadaqa ga yan uwa kuma yana hani game da alfasha da mummunan da dagawa da haka yake maku wa'azi koda zakuyi tunani"[62].

An karbo kuma daga Nu'umanu dan bashir Allah ya kara masu yarda yana kan minbari yace: " babana ya bani kyauta sai mahaifiyata Amratu diyar rawaha tace bazan yarda da wannan kyauta ba har sai manzon Allah s.a.w ya shaida da hakan sai mahaifina ya tafi gun manzon Allah s.a.w domin yashaida sai yace nayima yarona kyauta na wurin Amrata yar rawaha sai ta umurceni dana zo ka shaida hakan ya manzon Allah sai yace masa kaba sauran yaran naka irin wannan kyautan suma sai a'a sai manzon Allah s.a.w yace kuji tsoron Allah ku rika yin adalci a tsakanin yaran ku sai ya dawo gida na kwace wannan kyauta"[63].

Ina musa fada cewa musulunci ya danne hankin mata?

Hakkin mace na zabin mijin da takeso:

Musulunci ya girmama ra'ayin mata wurin aure kuma yana daukan haka cikin sharuddan ingancin aure ya bata hakkin yarda ko kuma rashin yarda da wanda yazo neman auren ta, manzon Allah s.a.w yana cewa: " kada a aurar da bazawara har sai da izinin ta kuma kada a aurar da budurwa har sai an sanar da ita ta yarda, sai sukace ya manzon Allah ya zamu gane yardanta sai yace yardanta shine yin shirunta"[64].

Baya halatta ga mahaifinta ko kuma wanda yake riketa ya tilasta mata akan auren wani, ga wanda kuma aka aurar da ita ba tare da yardanta ba tana da hakkin neman a raba wannan auren saboda hadisin Kansa'u diyar Juzama al-ansari cewa mahaifinta ya aurar da ita tana bazawara kuma bataso sai ta tafi zuwa ga manzon Allah s.a.w sai ya raba auren[65].

Hakika fadakarwan annabi me daaraja suna nuni akan himmatuwa da yara mata da wahabcin girmama su da kyautata masu da biya masu bukatunsu ta fuska kebantacce, manzon Allah s.a.w yana cewa: " duk wanda yake da yara mata uku ko kuma yan uwa mata uku ko yara mata biyu ko kuma mata yan uwa biyu sai ya kyautata masu zamantakewa ya kuma ji tsoron Allah akan kiyaye hakkokin su zai shiga aljanna"[66].

Musulunci ya irga haimmatuwa da kula da mata da kuma kyautata masu a matsayin ayyuka wanda suke sabbaba shiga aljanna domin hakan ya zama zaburarwa ga iyaye wurin himmatuwa dasu saboda kwadayin abunda ke wurin Allah na lada da sakamako, an karbo hadisi daga Aisha uwar muminai Allah ya kara mata yarda tace: " wata mata miskiniya tazomun tan rike da yara mata biyu sai na ciyar dasu da dabino guda uku, naba ko wanne a cikin su dabino daya ya kuma mika masu wannan dabino zuwa ga bakin su domin suci, sai wannan mahaifiyar tasu yakicin nata dabinon ta rabashi gida biyu ta karama yaranta sai hakan ya burgeni na ba manzon Allah s.aw labarin haka sai yace: " lallai Allah ya bata aljanna da wannan dabino, ko kuma ya yantata daga wuta da wanann dabino"[67].

Kamar yadda shari'a tayi umurni da daidaito da adalci tsakanin yara maza da mata wurin abubuwa wanda ake gani haka kuma yayi umurni dayin adalci wurin abubuwan kudi baya halatta ka fifita namiji akan mace ko kuma mace akan namiji cikin yaranka wurin bada kyauta, an karbo daga Nu'umanu dan bashir Allah ya kara masu yarda yace: mahaifiya yamun kyauta da wani abu cikin dukiyar sa sai mahaifiyata amratu diyar rawaha tace: nib azan yard aba da wannan kyauta har sai manzon Allah s.a.w ya shaida hakan sai mahaifina ya tashi ya tafi wurin manzon Allah domin hya shaida akan wannan kyauta dayayimun sai manzon Allah s.a.w yace masa: " shin ka ba kowa cikin yaranka irin wannan kyauta?" sai yace: a'a sai yace: " kuji tsoron Allah kuyi adalci a tsakanin yaran ku" sai mahaifina ya dawo ya kwace wannan kyauta[68].

Umurnin adalci da daidaito be tsayaba kawai akan abubuwan da ake gani ba abun ya wuce har zuwa wasu daga cikin abubuwa kanana da mutum ma be basu muhimmanci ba musulunci yayi umurni dayin adalci tsakanin yara hatta a wurin sunbata, Anas ya rawaito hadisi Allah ya kara masa yarda: " wani mutum ya kasance yana zaune a gun manzon Allah s.a.w sai wani cikin yaran sa yazo wurin say a kamashi ya sunbace shi dai ya zaunar dashi a kan kafarsa, sannan sai ga wata yarinyar sa tazo sai ya dauketa ya zaunar da ita a gefen sa, sai manzon Allah s.a.w yace: " bayi adalci ba a tsakanin su. Watan a tsakanin yaron namiji da macen wurin sunbata"[69].

Ya dace muyi Magana kadan akan kula da marayu da kuma himmatuwa da al'amuran su tunda muna cikin Magana ne akan himmatuwar da musulunci yaba yara kasancewar marayu suna cikin rayuwa na hatsari wanda hakan zai iya sakasu su canza zuwa ga wani addini na daban matukar al'umma bata kula da hakkokin su kuma basa tashi tsaye da wajibobin su kuma basa dubi zuwa garesu d idon rahama da tausayi..

Hakika musulumci ya himmatu da al'amarin marayu maza da mata himmatuwa babba ta yadda ya sanya kula dasu da renon su ya zama wajibi akan yan uwan sun a jini, idan basu da yan uwa na jini ya zama wajibi akan gwamnatin kasa ta musulunci ta himmatu da harkokin su da tarbiyyar su da kuma daurasu akan hanya na gari.

Hakika kuma azaba me girma yazo daga Allah madaukai akan wanda yaci dukiyar maraya ya kuma toyarza hakkokin shi, Allah madaukaki yace: " lallai wanda sukecin dukiyar maraya da zalumci ba komai suke cima cikinsu ba face wuta, kuma da sannu zasu tarar da wutan sa'ir"[70].

Manzon Allah s.a.w kuma yace: " lallai ina jiye maku tsoro akan hakkokin maraya da mace"[71] albani ya hassana hadisin cikin alsahiha (1015) ma'anar hadisin shine manzon Allah s.a.w yana tabbatar da kunci da zunubi ga mutumin daya tozarta hakkokin su ya kuma zalumce su da cutar dasu.

 Kamar yadda tsoratarwa ya gabata akan tsawatar dasu da kuma Koran su, Allah madaukaki yace: " maraya kuma kada ka koreshi (9)"[72]. Nassoshi da dama na shari'a sunzo wanda suke kwadaitarwa akan daukan nauyin maraya da kuma kyautata masa, manzon Allah s.a.w yace: " ni da wanda ya dauki nauyin mara kamar haka muke cikin gidan aljanna sai yayi nuni da yatsunsa na tsakiya dame tsokanan fada ya hada tsakanin su"[73].

Haka kuma kwadaitarwa yazo akan su akan tausaya masu da jin kansu, manzon Allah s.a.w yana cewa: " kanason zuciyar ka tana taushi kuma ka samu bukatunka? To kaji tausayin maraya kuma ka shafi kansa kuma ka ciyar dashi daga abincin ka, zuciyar ka zatayi taushi kuma za'a samu bukatarka"[74].

Kamar yadda musulunci ya himmatuhar wayau da yaran da aka tsinta namiji ne ko mace daga cikin hakkin su a muslunci da kuma kasa ta musulunci shine himmatuwa dasu kamar marayu, manzon Allah s.a.w yana cewa: "…cikin ko wani hanta danye watan ko wnai me rai idan ka ciyar dashi ko shayarwa kanada lada"[75] da wannan aiki na himmatuwa dasu zai zama mun samarma al'umma mutane na kwarai wanda zasu rika sauke nauyin su na kasa da kuma rayuwa daidai da ta mutane.

 

 

Hakkokin mace cikin musulunci a matsayin matan aure:

Allah madaukaki yace: " kuma yana daga cikin ayoyin say a halatta maku mata daga kawunan ku domin ku samu natsuwa zuwa garesu ya kuma sanya soyayya da rahama a tsakanin ku, lallai cikin haka akwai ayoyi ga mutane masu tunani (21)"

(suratul rum ayata 21)

Daga cikin ayoyin sa wanda yake nuni zuwa ga girman sa shine ya halattama mutum mata daga jikinsa domin sashin su su samu natsuwa da sashi kuma su samu kwanciyar hankali na jikinsu na kwanciyar zukatan su.

Matan aure a musulunci itace ginshiki na al'umma wanda suke ginuwa akai da kuma turaku na asali wanda ake daura ginin gidan musulunci akan sa musulunci ya wajabta mata hakkoki da wajibobi sannan itama ya wajabta hakan akanta, daga cikin hakkokinta da wajibobinta:

Hakkinta na sadaki:

Sadaki hakki ne na wajibi da kyauta ta dole wanda musulunci ya daurama miji yaba mace, baya halatta ga wanda yafi kusanci da ita ya amshi wannan sadaki cikin mutane ba tare da yardanta ba da amincewarta kuma aure baya dauruwa sai dashi, wannan dalili ne wanda babu shakka acikin sa akan hakkin mace na mallakar dukiya, sannan kuma wannan sadaki baya fadi koda kuwa matar ta yarda da hakan har sai bayan daurin aure idan an daura aure to tanada yancin yin abunda taga dama da abunda ta mallaka yadda takeso, Allah madaukaki yace: " kuba mata sadakin su kyauta a garesu, idan sun tsakura maku wani abu daga cikin na dason ransu to kuci halak malak dinku ne (4)"

(suratun nisa'i ayata 4)

  • Sadaki hakki ne na mace baya halatta ga miji idan ya rabu da ita kuma sakin ya zama daga wurin sa ne ya amshi wani daga cikin sadakin ta wanda ya bata, kuma hakika Allah madaukaki ya bayyana haka kyamar haka da munin wannan abu, Allah madaukaki yace: " idan kuma kuna son canza wata mata wurin wata matar taku kuma kun ba daya daga cikin su sadaki na dukiya me tarin yawa to kada ku amshi komai daga cikin, zaku amsa ne domin zalumci da zunubi bayyananne (20) taya zaku amsa bayan kun sadu da juna kunji dadi da juna kuma an dauki alkawri me kwari daga gare ku (21)"

(suratun nisa'i ayata 20-21)

Kuma Allah madaukaki yana cewa: " yaku wanda sukayi imani baya halatta da ku rika gadon mata ta dole bada yardan su ba, sannan kuma kada ku hanasu tafiya da wani daga cikin abunda kuka basu sai dai idan sunzo da alfasha ne bayyananne, ku zauna dasu da kyautatawa idan kuma kun kyamaci su to zaku iya kyamatan abu kuma Allah yasanya masa alheri dayawa (19)"

(suratun nisa'i ayata 19)

A cikin wannan aya me girma akwai lamuni ga hakkokin matan aure wanda Allah madaukaki ya bayya kamar haka:

  • Haramcin gadar mace basaso, hakika larabawa sun kasance gabanin zuwan musulunci kamar yadda ya gabatan mana cewa idan mutum yam utu sai yan uwansa ya gaje matar sa idan wasu sunso a cikinsu sai su aureta ko kuma su aurar da ita ga wanda suke so ko kuma idan sun so suyi banza da ita su basu aureta ba kuma basu kyaleta ba ta aure wani sais u riketa sunfi hakki da ita akan iyalanta ta zama kamar wata haja wacce suka mallaketa cikin gado.
  • Sa'annan Allah madaukaki ya bayyana haramcin miji ya kaurace matar sa domin ya cutar da ita da kuma gallaza mata kamar zagi ko kuma duka ko cin dukiyar ta ko kuma ya hanata fita da makamantan su saboda cucarwa a gareta domin ta fanshi kanta da kudi idan tanason ya rabu da ita.
  • Kuma musulunci ya halastawa miji aikata hakan idan mace ta zo da alfasha watan "zina" har sai miji ya amshi sadakin sa daya bata daganan sai ya rabu da ita ta hanyar saki.
  • Sai kuma Allah madaukaki yayi umurni da wajabcin zama kyautata zama da mace da kuma tausayi da kuma jiyar da ita magana irin wanda take so da kuma aikin da ta yarda dashi.

Hakkin matan aure na daidaito da kuma adalci:

Wannan idan mijin yanada mata sama da yada kenan ya wajaba a gareshi dayin adalci a tsakanin su na abinci da abunsha da tufafi da wurin zama da kwanciya, manzon Allah s.a.w yace: " duk wanda yake da mata biyu sai ya karkata zuwa ga daya acikin su zaizo ranan alkiyama da shanyayyen daga daga cikin barin jikin sa"[76].

Hakkinta na ciyarwa:

Ya wajaba akan miji ya ciyar da matar sa gwargwadon halin sa da kuma bata mazauni wanda ya dace da kuma biya mata bukatunta na ci da dasha da tufafi koda kuwa me arkizi ce, manzon Allah s.a.w yana cewa: " kuji tsoron Allah game da mata domin lallai kun amshe su ne cikin kariyan Allah kuma kuma halasta farjin su da Kalmar Allah, sannan kuma kuna da hakki akansu na kada su kwanda da wani akan gadonku abunda bakwaso idan kuma sun aikata hakan ku duke su duka ban a cutarwa ba, sannan kuma ciyarwan su da tufatar dasu yana kanku ne dai dai gwargwado…."[77]

Kuma ya rika bata kudi daidai abunda take bukata gwargwadon halin sa da karfin sa, Allah madaukaki yace: " me dukiya ya ciyar daga cikin yalwan sa wanda kuma bashi da yalwa na dukiya ya ciyar gwargwadon abunda yake dashi Allah baya daurama rai sai abunda ya bata da sannu Allah zai sanya sauki bayan tsanani (7)"[78].

  • Idan miji me wadata ya hana matar sa abinci kuma yanada shi to matar tana dana da damar daukan abunda zai isheta da yaranta ba tare da barnaba cikin kudinsa ba tare da izinin sa ba saboda hadisin hindu yar utubata tace: ya manzon Allah lallai mijina abu sufyan mutum ne me mako baya bani abunda zai isheni da yarana sai dai na dauka dakaina ba tare da saninsa ba, sai manzon Allah yace mata: " ki dauki abunda zai isheki ke da yaranki ba tare da barn aba"[79].
  • Idan miji ya gagara ciyar da matar sa ko kuma ya bace ba'asan inda yake ba kuma matar tana cutuwa saboda rashin wanda zai ciyar da ita kuma yaki dawowa tana da damar neman a raba wannan auren idan taso haka, an karbo daga abiz-zinad yace: na tambayi sa'ad dan musayyab game da mutumin da bai samu abunda zai ciyar da matar sa ba? sai yace: sai a raba auren su. Sai abuz-zinad yace: wannan sunnar manzon Allah ce s.a.w? sai sa'id yace: eh sunnanr manzon Allah s.a.w ce, shafi'i yace abunda maganar sa'ida ke kama dashi na cewa sunna ce shine ta kasance sunnar ce cikin sunnar manzon Allah s.a.w.[80]

Hakkinta na wurin kwana da kuma rayuwan aure:

Wannan yana daga cikin hakkoki masu muhimmanci wanda shari'a yake umurtan miji dashi da kuma kiyaye shi saboda kada mata ta fada cikin wani yanayi wanda karshen sa babu kyau, a matsayinta na mata tana da bukata na zuciya wanda zai rika tausayinta da lallashinta da kuma namiji wanda zai rika mata wasa wanda zai rika dauke mata kewa da biya mata bukatarta na sha'awa, kuma hakika shari'a ta haramta dulmiya cikin ibada tsanya domin cika wannan wajibin saboda hadisin salmunul farisi Allah ya kara masa yarda: yazo gun abuldarda'i Allah ya kara masa yarda domin masa ziyara sai ga ummu darda'i dashiga ta rashin ado sai yace mata na naganki haka ke kuma? Sai tace dan uwanka baya bukatata a duniya, yana sallan dare kullum kuma da rana yayi azumi!! Sai abuddarda'i yazo yayi masa maraba, ya kawo masa abinci sai salman yace masa: muci to. Sai yace masa: ni ina azumi, sai yace nayi rantsuwa sai ka karya shi, sai sukaci abincin tare, sai ya kwana a wurin sa, a lokacin da dare yayi abuddarda'I yanason yin salla sai salmanu ya hanashi, yace: lallai jikinka yanada hakki akanka sannan kuma ubangijinka yanada hakki akanka kuma iyalinka tanada hakki akanka, kayi azumi yau gobe ka huta, kayi salla sannan ka kusanyi iyalinka, kaba kowa hakkinsa, a lokacin da asuba ta kusa sai yace masa: tashi to yanzu idan kanaso, sai ya tashi yayi alwalla sa'annan yayi salla, sannan suka fita zuwa sallar asuba, sai manzon Allah s.a.w yazo sai yabashi wannan labari sai manzon Allah s.a.w yace: lallai salmanu yayi gaskiya"[81].

Ibn hazam yace: an wajabta akan miji daya sadu da matar sa akalla cikin ko wani tsarkinta sau daya idan yanada ikon haka idan kuma yaki to ya sabama Allah amdaukaki… dalilin haka kuma shine fadin Allah madaukaki: " idan sunyi tsarki to kuzo masu ta inda Allah ya umurce ku".

  • Daga cikin hakkinta akan mijinta shine idan zayyi tafiya to kada ya wuce watanni shida idan kuma tayi hakuri akan wuce haka ta janye daga hakkinta babu laifi hakan idan ya kasance sha'awarta me rauni ne idan kuma ba haka ba ya wajaba a gareshi ya dawo a duk lokacin da ta nemi haka kuma kada yayi jinkira sai idan da dalili ne wanda yafi karfinsa, saboda aikin Umar dan kaddab Allah ya kara masa yarda khalifar manzon Allah s.a.w na biyu lokacin daya ji wata mata tana cewa:

Wannan dare yayi tsayi kuma gefensa yayi duhu***

                        Kuma gashi babu wani aboki wanda zanyi wasa dashi.

Na rantse badan Allah yana ganina ba***

                        Dana jijjiga wannan gado da wani mutum.

Bayan gari yaw aye sai Umar ya aika akirata sai yace mata: kece kikace kaza da kaza? Sai tace: eh nice, sai yace: saboda me to kika fadi hakan? Sai tace: ka tura mijina yaki, sai yace: sai Umar ya tambayi Hafsa wata nawa ne mace zata iya hakuri bata sadu da mijinta ba? Sai tace masa: wata shida, daga Umar ya kasance yana dawo da sojojin sa gida duk bayan wata shida[82].

  • Tsare mata sirrinta da kuma boye aibinta ga kowa da kuma boye abunda yake gani ko kuma daga hareta na alakar su ta aure kada ya rika bada labarin haka ga abokan sa a majalisa, manzon Allah s.a.w yace: " lallai daga cikin tantiran mutane a wurin Allah ranan alkiyama sune mutumin da zai sadu da matar sa sannan kuma dayan su yazo yana yada sirrin abokin sa"[83].

Hakkinta na zama da ita me kyau da kuma kyautata mata mu'amala:

  • Daga cikin hakkinta yi mata mu'amala me kyau da kuma darajata koda kuwa ya kwamaci wani abu daga gareta, Allah madaukaki yana cewa: " kuyi zama dasu da kyawawan mu'amala idan kuma kun kyamace su to zaku iya kyamatan abu sai Allah yasa masa alheri me yawa (19)"[84].

Idan kuma mutum baya sonta baya halatta ya wulakantata ko kuma kasakntar da ita ya wajaba a gareshi ya riketa da rahama da tausayi da rangwanta mata ko kuma ya rabu da ita tare da kyautata mata, Allah madaukaki yace: " saki sau biyu ne kodai ka rike ta da kyautatawa ko kuma ka rabu da ita da kyautatawa"[85].

Kasancewar kamala abu ne wanda bazai taba yuwa ba ga mata, manzon Allah s.a.w yana cewa: " ina maku wasiyya da kyautata ma mata, domin mace an halicce ta ne daga kashin hakarkari na sama kuma kuma kashin dayafi karkace a hakarkarin mutum wa shine kashin sama ikan kaje zaka mikar dashi zaka karya shi idan kuma ka kyaleshi bazai gushe ba a karkatanshi saboda haka ku rike su cikin tausayi da kyautatawa"[86].

Saboda kasancewar kuskure dole ne cikin zamanta kewar ma'aurata an umurci miji dayin hakuri da kuma juriya daga abunda zai gani daga wurin matar sa wanda baya so saboda kiyaye rayuwan aure, ya zama wajibi a gareshi idan ya tuna laifinta sai ya tuna alherinta, manzon Allah s.a.w yana cewa: " kada mumini ya kyamace mumina baki daya, idan bayason wasu halaye nata zaiga wasu halaye nata daya yarda dasu "[87].

  • Tausayi da rangwanta mata da lallashinta, manzon Allah s.a.w yana cewa: " wanda yafi muminai cikin imani shine wanda yafi su kyawawan hali kuma wanda yafi matsayi a wurin Allah shine wanda yafi ku matsayi agun matansa"[88].
  • Yin wasa da ita da tsokana da bata dariya, an karbo daga Aisha Allah ya kara mata yarda tace: manzon Allah s.a.w yayi tsere dani sai na tsere masa bayan nayi kiba sai muka kara yin tsere sai ya tsere mun sai manzon Allah s.a.w yace: "wannan ramuwa ce akan wancan lokaci"[89].

Musulunci ya irga hakan cikin hakki, manzon Allah s.a.w yace: "duk wani wanda baya cikin ambaton Allah to lagawu ne ko kuma wasa mara amfani sai abu hudu kawai: koyan harbi da koyan hawan doki da wasa da iyali da koyan nunkayan ruwa"[90].

  • Kiyaye dikiyanta kada yayi mata amfani dashi sai da izininta kuma baya halatta ya dauki wani abu daga ciki sai da yardanta da kuma saninta, Allah madaukaki yace: " kada ku rikacin dukiyoyin a tsakanin ku da barna"[91].
  • Yin shawara da ita cikin al'amuran da suka shafi gida da yara da abunda yake tsakanin miji da mata wanda suke tarayya aciki.

Baya cikin hikima mutum ya kaurace ma ra'ayin matar sa da rashin amsar ra'ayinta idan ya kasance daidai, shawara yana cikin abunda ko wannen su ya wajaba ya rike nema agun dan uwansa, Allah madaukaki yana cewa: " kuma al'amarin su na shawara ne a tsakanin su"[92].

  • Taimaka mata da ayyukan gida da kuma kin aikatawa haka domin kuwa manzon Allah s.a.w ya kasance hana dinke tufafin say a kuma gyara takalmin sa da taimakon matan sa cikin wasu ayyukan gida, an tambayi Aisha cewa: menene manzon Allah s.a.w yake aikatawa agidansa? Sai tace: ya kasance yana cikin hidimar matar sa watan taya su aikace aikace har idan lokacin salla yazo sai ya fita zuwa masallaci.[93] Manzon Allah ya kasance mana abun kuyi na kwarai.
  • Tunkaho da neman ganin kaskancinta da kuma bibiyan laifukanta, manzon Allah s.a.w yana cewa: " idan dayanku yayi tafiya ya dade bayanan to kada ya dawoma matar sa cikin dare ko kuma ya shigo mata gida babu sanarwa"[94].

Saboda kada yaga matar sa cikin wani yanayi wanda bazai burgeshi ba sai ya zama sababi na kyamarta.

  • Ya nisanci cutar da ita koda da magana ne wanda zai zubar da mutuncinta da kuma bata mata rai, saboda fadin manzon Allah s.a.w ga wanda ya tambayeshi yace: ya manzon Allah menene hakkin matan mu akan mu? Sai yace:" ya ciyar da ita irin abunda yaci kuma ya tufatar da ita idan ya tufatar da kansa kuma kada ya duke ta a fuska kuma kada ya zageta ko kuma fada mata magana mara kyau kuma kada ya kaurace mata sai acikin gida kawai"[95].
  • Tana da hakki idan taji batason mijinta ta nemi ya saketa amma da sharadin zata mayar masa da sadakinsa daya bata sai dai abunda ya yafe mata daga ciki, an rawaito hadisi daga ibn Abbas cewa: " lallai Jamila diyar Salul tazo gun manzon Allah s.a.w sai tace: wallahi ya manzon Allah bana kin zaidu akan addinin sa ko kuma halayen sa sai dai ina tsoron kafurci bayan shigata musulunci bazan iya masa biyayya ba saboda kinsa danake, sai manzon Allah s.a.w yace mata: " zaki mayar masa da gonar daya baki a matsayin sadakinki?" sai tace: eh, sai manzon Allah s.a.w ya umurce sa daya amshi wannan gonar tasa kuma kada ya nemi Karin wani abu akan haka sannan ya sake ta"[96].
  • Lula da ita dakyau abunda zai iya zama sababi na zubar mata da kima da kuma keta mutuncinta, manzon Allah s.a.w yane cewa: " mutum uku baza su shiga aljanna ba me sabama iyayensa da cutar dasu da mara kishin matarsa da kuma mace me kama da mazawurin shiga da sura"[97].
  • Kishi da kuma nesantar da ita daga wuraren sharri kada ya rike tunkudata zuwa wurin barna da hauka da cudanya maza da mata, manzon Allah s.a.w yana cewa: " lallai Allah yana kishi kuma mumina ma yana kishi kishin Allah itace mumini ya aikata abunda Allah ya haramta"[98].

Sai dai wannan kishin dole ne ta ksance na hankali, manzon Allah s.a.w yana cewa: " lallai daga cikin kishi akwai wanda Allah yakeso kuma akwai wanda Allah bayaso, irin kishin da Allah yakeso ita kihi cikin dukkanin wuraren barna idan alamomin hakan ya bayyana, kishin kuma da Allah baya so shine kishi mara dalili na shari'a"[99].

 

 

 

Hakkokin mace a musulunci a matsayinta ta uwa:

Musulunci yayi wasilci ga kyautatawa iyaye cikin ayoyi dayawa na qur'ani kuma Allah madaukaki ya hada hakkinsa dana iyaye saboda nuna girman hakkinsu da kuma falalar su, Allah madaukaki yace: " kuma ubangijinka ya hukunta cewa kada ka bautawa kowa sais hi kadai kuma iyaye ka kyautata masu idan daya daga cikin su yayi tsawon kwana tare dakai ko kuma dukan su biyun kada kace masu tir kuma kada ka rika masu tsawa ka rika fada masu magana ta girmamawa (23) ka kuma shinfida masu fuka fukanka na rahama kuma kace ya Allah ka masu rahama kamar yadda suka reneni ina yaro (24)"[100] .

  • Musulunci ya sanya kyautatawa iyaye da masu biyayya da kuma rashin cutar dasu da kankan masu dakai da nuna masu soyayya cikin sababi na shiga aljanna, Jahima yazo gun manzon Allah s.a.w sai yace: ya manzon Allah s.a.w inason na fita yaki nazo neman shawaranka ne, sai manzon Allah s.a.w yace masa: " kanada mahaifiya?" sai yace: eh inada ita, sai manzon Allah s.a.w yace masa: " kaje ka zauna da ita domin lallai aljannarka yana karkashin kafafuwanta"[101].

Kasancewar mace a mafiya yawan lokuta itace me rauni cikin al'umma wanda hakan zai iya sanya mantawa da ita da kuma toye dayawa daga cikin hakkokinta sai musulunci ya gabatar da ita akan mahaifi wurin biyayya da kuma kyautatawa da tausayi da zama me kyau dagewa wurin kyautata mata da kyuta saboda ya toshe kofa na toye hakkokinta, an karbo daga abi huraira Allah ya kara masa yarda yace: " wani mutum yazo wurin manzon Allah s.a.w sai yace: ya manzon Allah wanene yafi kowa cancanta da kyautata zama dashi a guna cikin mutane? Sai manzon Allah s.a.w yace: mahaifiyar ka, sai mutum yace: sai kuma wane? Sai yace mahaifiyarka, sai ya kara cewa: sai kuma wane? Sai yace sai mahaifiyar ka, sai kuma ya kara cewa: sai kuma wane? Sai yace sai mahaifinka"[102].

Abunda wannan hadisi ya kunsa shine kamar yadda akayi sharhi shine ya kasance mahaifiya tana da nunki uku na mahaifi wurin biyayya saboda wahalar cikin da tayi da haihuwa da shayarwa, wannan abubuwan guda uku sune wanda mahaifiya ke kebanta dasu sannan kuma tana tarayya da mahaifi wurin tarbiyya.

Mahaifiya tana daukan cikinki kayi rayuwa karkashin abincinta da lafiyarta na tsawon wata tara mafiya yawa sa'annan kuma ta shayar dakai na tsawon shekara biyu ga wanda takeson kaiwa hakan kamar yadda ubangijin mu ya nuna hakan cikin fadin sa cewa: "munyima mutum wasiyya da kyautatawa iyayensa, mahaifiyar sa ta dauki cikin sa cikin wahala kan wahala kuma ta shayar dashi na tsawon shekar biyu lallai ka gode mani da iyayen ka, gareni makoma take"[103].

Musulunci ya hana cutar da iyaye da kuma saba masu cikin umurni da rashin bayar da hakkokin su, manzon Allah s.a.w yace: " lallai Allah madaukaki ya haramta maku cutar da iyeye mata da kuma hanaku kin ciyar dasu da bayar da zakkan daya wajaba agareku da tambaya da neman abunda baka da hakki aciki, da birne yara mata da ransu, ya kyamatan maku ance kace, da yawan tambaya da barna da kudi"[104].

  • Yi mata biyayya da aikata abunda tayi umjrni da kuma kin saba mata matukar batayi umurni ba da sabawa Allah, idan tayi umurni da sabawa Allah to baza'a mata biyayya ba cikin haka saboda yardan Allah tana gaba da yardanta sannan kuma biyayyar Allah tana gaba da biyayyar ta amma kuma hakan bayana nufin zai munana mata ladabi bane na tsawatar mata da daga murya a'a anason ya tausasa mata kuma yayi mata bayanin haka cikin sanya da dabara kamar yadda ubangiji madaukaki ya bayyana cikin fadin sa cewa: " idan sun nema daga gareka da kayimun shirka da abunda da baka da ilimi akai to kada kayi masu biyayya cikin haka ka zauna dasu a duniya da maza me kyau kuma kabi hanyar wanda kake komawa zuwa gare sa, sa'anan gareni makomar ku take zan baku labari akan abunda kuka aikata (15)"[105].
  • Domin ubangijin mu madaukaki ya bayyana girman hakkin iyaye a garemu sai ya sanya yardan sa cikin yardan su, sannan kuma fishin yana tare da fishin su, saboda ya kwadaitar da yara akan yaruwa na mutunci da kajara tare dasu, manzon Allah s.a.w yana cewa: " yardan Allah tana tare da yardan mahaifi sanann kuma fushin Allah yan atare da fushin mahaifi"[106].

Yardan su da kuma biyayyar su sababi ne na shiga aljanna sannan kuma fushin su da cutar dasu sababi ne na shiga wuta kamar yadda manzon Allah s.a.w ya bayyana, an karbo daga Anas Allah ya kara masa yarda yace: an tambayi manzon Allah s.a.w manyan laifuka sai yace: " shirka da Allah da kuma cutar da iyaye da kashe rai da shedar karya"[107].

An karbo daga Abdullahi dan umar yace: manzon Allah s.a.w yace: " yardan ubangiji yana cikin yardan mahaifi sannan kuma fushin Allah yana tare da fushin mahaifi"[108].

An karbo kuma daga abuddarda'i yace: naji manzon Allah s.a.w yana cewa: " mahaifi ne shine shamakin kofar aljanna saboda haka ka kiyaye iyayen ka ko kuma ka bari"[109].

  • Musulunci ya gabatar da biyayyar iyaye akan ayyukan nafiloli na salla da makamantan su, an karbo daga abi huraira Allah ya kara masa yarda daga manzon Allah s.a.w yace: " babu wanda yayi magana yana cikin tsummar goyon sa cikin mutane sai mutum uku: Isah dan Maryam amincin Allah su tabbata a gareshi, kuma ya kasanci cikin bani sira'ila akwai wani mutum wanda kae kira da juraij ya kasance mutum ne me yawan bauta, ya gina bukka yana zaune a ciki sai mahaifiyar sa tazo wurin sa yana salla sai tace: ya juraij, sai yace: ya ubangiji na mahaifiyata tana kira ina cikin salla sai yaci gaba da sallar sa sai ta tafi. Washe gari sai ta kara dawowa yana salla sai tace: ya juraij sai yace: ya ubangiji mahaifiyata tana kirana kuma ina salla sai yaci gaba da sallar sa, washe gari kuma sai takara dawowa tazo yana salla, sai tace ya juraij sai yace ya ubangiji mahaifiyata tana kirana kuma ina salla, sai yaci gaba da sallar sa sai mahaifiyar tace: ya Allah kada ka kashe har sai ka nuna masa wata karuwa wacce zaka masa kazafi. Bani isra'il sun kasance suna ambaton juraij da ibadar sa, sai wata mata karuwa wanda ake misali da kyawunta sai tace masu: idan kunso zai jarabci ibadar sa, sai tazo wurin sa be kulata ba , sai wani me makiyayi yazo wanda yake kiwo kusa da wannan bukka tashi sai ta yaudare shi yayi amfani da ita ta samu ciki, bayan ta haihu sai tace: wannan yaron juraij ne, sai suka zo suka tafi dashi suka rusa wannan bukka nashi suna dukan sa, sai yace meke damunku ne? sai sukace kayi zina da karuwa ta haifan maka yaro, sai yace: ina yaron yake? Sai suka zo dashi, sai yace: ku kyaleni nayi salla, bayan y agama sallar sai yazo gun jaririn ya mintsilesa a ciki sai yace masa: ya kai wannan jariri wanene babanka? Sai jariri yace: wane ne babana wannan makiyayin, sais u koma suna sunbatar jurair suna shafansa suna cewa: kana son mu gina maka bukkanka na zinari, sai yace: a'a kada ku ginamun da zinari kudai ginamun da kasa kamar yadda yake, sai suka gina masa…."[110].

Hasalima ya sanya biyayyar su gaba da jihadi domin daukaka addinin Allah matukan bai zama wajibi ba akan kowa, an karbo daga Abdullahi san Amru dan Aas Allah ya kara masu yarda yace: wani yazo yazo gun manzon Allah s.a.w sai yace: inyi maka mubaya'a akan yin hijira da jihadi fisabilillah ina me neman lada a wurin Allah madaukaki, sai manzon Allah s.a.w yace masa: " kanada daya daga cikin iyayenka a raye?" sai yace: eh dukansu suna raye sai yace masa:" kana neman lada daga wurin Allah madaukaki?" yace: eh, sai yace masa: " to ka koma wurin iyayeynka ka kyautat zama dasu"[111].

  • Kasancewar musulunci yazo ne domin karfafa alaka tsakanin mutane bawai yanke alaka atsakanin su ba, saboda haka ya wajabta kyautatawa iyaye da kudi da basu kyauta da kalma me kyau da zama dasu me kyau koda kuwa addini ba daya bane, an karbo daga Asma'u Allah ya kara mata yarda tace: mahaifiyata tazo guna kuma ita mushrika ce sai na tambayi manzon Allah s.a.w nace: mahaifiyata tazo guna kuma tanason na rika ziyartarta shin zan iya ziyartarta? Sai manzon Allah s.a.w yace: " eh ki rika ziyartarta"[112].
  • Kuma domin a kwadaitar da musulmi akan himmatuwa da iyayen sa manzon Allah s.a.w ya bayyana cewa lallai biyayyar su da kyautata masu sababi ne na Allah ya amsama mutum addu'ar sa, manzon Allah s.a.w yana cewa: " wasu mutane uku sunyi tafiya cikin mutanen da suka gabace ku har sukaje cikin wani kogo domin kwana aciki bayan sun shuga sai wani dutse yazo ya rufe su a ciki sai sukace lallai babu abunda zai tsiratar damu daga cikin wannan kogo face mu roki Allah da ayyukan mu na kwarai, sai wani mutum acikin su yace: ya Allah inada iyaye guda biyu tsofaffi na kasance bana gabatar da kowa akansu wurin shayar dasu madara da daddare sai wata rana na shagaltu nayi nisa da gida domin neman wani abu na makara ban dawo bhar sai da sukayi bacci sai ya tatso masu madaransu na dare koda naje sai na tarar da sunyi bacci sai na kyamaci na gabatar da wannan madara ga iyalai na akansu ko kuma dukiya ta sai na zauna da kwaryan a hannuna ina jiransu su farka har alfijir ya fito sannan suka tashi na basu suka sha, ya Allah idan nayi wannan ne dominka ka yaye mana wannan hali da muke ciki a cikin wannan kogo sai ya bude kadan amma babu wanda zai iya fita ta wannan kofa, sai manzon Allah s.a.w yace sai dayan shima yace ya Allah na kasance inada wata yarinyar baffana na kasance ina matukar sonta sai na nemi yin lalata da ita taki har sai da farin abinci ya samesu sai tazomun na bata dinari dari da ashirin akan ta bani kanta nayi zina da ita, ta yarda har sai da nagama himma akan haka mun zo zamu kanta sai tacemun kada ka kuskura ka huda zuben da banaka sai wannan magana tamun tasiri na kyaleta kuma ina makukar kaunarta kuma nabar mata zinarin dana bata ya Allah idan nayi hakan ne domin k aka yaye mana wannan hali da muke cikinsa sai wannan dutse ya kara budewa kadan amma babu wanda zai iya fita a ciki sai manzon Allah s.a.w yace sai mutumin na uku yace ya Allah na taba dauko hayan ma'aikata bayan sun gama aiki na biyasu daukan su sai wani mutum daya a cikin su banganshi ba sai na ajiye masa kudin sa naci gaba da jujjaya masa bayan shekara me tsayi sai ga wannan mutumi yazo yace ina kudina na aikin dana taba yima maka sai nace masa shiga ka kunce wancan garken na awakai lallai kudin ka ne ya siya akuya daya da ita nata kiwata maka har sukayi yawan haka ya Allah idan nayi wannan abune dominka ka yaye mana wannan hali da muke ciki sai wannan dutse ya bude baki daya suka fito suka tafi"[113].
  • Musulunci ya sanya yi masu biyayya da kyautata masu cikin kaffara daga zunubai da kuma abunda Allah yalke share zunubai dashi, an karboda daga Abdullahi dan Umar Allah yakara masu yarda yace: wani mutum yazo gun manzon Allah s.a.w yace: ya manzon Allah nayi zubnubi masu yawa shin inada wani abu da zan aikata domin tuba? sai manzon Allah s.a.w yace masa" kanada iyaye a raye?" sai yace: a'a bana dasu. Sai yace to kanada kanwa ko kuma yar mahaifiya? Sai yace eh inada su, sai yace: " to kayi mata biyayya"[114],
  • Hakan ya faru ne saboda inna a musulunci a matsayin mahaifiya take, saboda fadin manzon Allah s.a.w: " inna tana matsayin mahaifiya ce"[115].

Kuma hakika musulunci ya sanya hankin iyaye me wanzuwa hatta bayan mutuwar su, an karbo hadisi daga abi huraira manzon Allah s.a.w yace: " idan mutum yam utu dukkanin ayyukan sa sun tsaya sai guda uku, sadaka me gudana ko kuma wani ilimi wanda ake amfanuwa dashi ko kuma yaro nagari wanda zai zika masu addu'a"[116]

 

 

 

Hakkin mace a musulunci a matsayinta na mace kamar sauran mata:

An wajabtawa musulmai kyautatawa mace da kuma yi masu alheri, saboda fadin manzon Allah s.a.w: " lallai mumina da mumini kamar gini ne sashi yana karfafa wani sashi sai daure yatsunsa biyu da juna"[117] .

  • Idan mace ta kasance goggo ko kuma inna ko yar uwa to tana cikin yan uwa na mahaifa wanda Allah yayi umurni da arika ziyartar su sannan kuma yayi alkawarin azaba ga wanda ya yanke daga ziyartar su, Allah madaukaki yace: " shin kuna tsammani ne idan kuka juya baya zakuyi barna a doron kasa kuma ku yanke zumuncin ku (22)"[118].

Manzon Allah s.a.w yana cewa: " me yanke zumunci bazai shiga aljanna ba"[119].

Kuma ya irga kyautata masu cikin ayyukan da ake ba musulmi lada akai sau biyu, manzon Allah s.a.w yace: " sadaka ga miskini lada day ace sannan ga dan uwa kuma lada biyu celadan sadaka da kuma na zumunci"[120].

  • Idan kuma sun kasance daga cikin makwabta sun kasance suna da hakki biyu kenan, hakkin musulunci da hakkin makwabtaka, Allah madaukaki yace: " ku bautawa Alah kada ku hadashi da wani cikin bauta sannan kuma ku kyautatawa iyaye da yan uwa da marayu da miskinai da makwabta cikin yan uwa da makwabta na gefen ka"[121]

Ya wajaba akan makwabcinta daya kyautata mata kuma ya rika biyayar halinta yana biya mata bukatunta na harkokin yau da kullum ya kuma rika taimaka mata da abunda take bukata, manzon Allah s.a.w yace: " mala'ika Jibril bai gushe ba yana mun wasiyya akan makwabci har sai da nayi tsammanin za'a bashi gado"[122].

Kamar yada yake wajaba a garesu da su kame daga cutar da ita , manzon Allah s.a.w yana cewa: " wallahi beyi imani ba, wallahi beyi imani ba, wallahi beyi imani ba sai akace wanene wannan ya manzon Allah? Sai yace: " duk wanda makwabcinsa be tsiraba daga sharrinsa"[123].

  • Domin musulunci ya lamunce hakkokin mace ya kuma sanya hidimarta da biya mata bukata cikin ayyukan da musulmai ake rigegeniya akai sai ya irga tafiya domin biyan bukatu akan mata mabukatu cikin ayyuka masu falala, manzon Allah s.a.w yace: " tafiya domin bukatar mace gajiyayyiya da miskinai kamar me jihadi ne fisabilillahi ko kuma me sallar dare kullum da azumi kullum"[124].

Sahabbai Allah ya kara masu yarda sun kasance suna bibiyan halayen makwabtar su mu samman ma mabukatan cikin su da mata, an rawaito daga Dalhata Allah ya kara masa yarda yace: " Umar dan kaddab ya fita cikin wani dare yana shugaban muminai sai ya shiga wani gida sannan ya kara shiga wani gida kuma bayan asuba tayi sai ya wuce ta wanann gida sai na shiga ciki sai naga wata tsohuwa makauniya a zaune bata iya tashi, sai nace mata: menene labarin mutumin jiya sai tace: " mutum ne wanda yake hidima dani kullum tun lokaci kaza yana biyamun bukatuna sannan kuma ya tsabtacemun gida nay a kuma mun tsarki, sai Dalhatu yace: tab yanzu shin har akwai gazawan umar da zamu rika bibiya?"[125].

Wata kila abunda muka ambata abaya mun Ambato ne a gurguje daga cikin hakkoki da wajibai wanda akarkashin su akwai wasu hakkoki da wajibai na daban da bamu ambata ba saboda tsoron kada mu tsawaita sannan kuma mu bayyanawa me karatu wasu daga cikin surori masu haske na girmama mace da karramata a musulunci wanda duniya bata ganshi ba a baya can ko a yanzu irin wannan girmamawan da da karramawa kuma ba'a taba gani ba sai a karkashin inuwar musulunci da kuma dabbaka hukunce hukuncen sa.

 

 

 

SHUBUHOHI GAME DA MACE A CIKIN MUSULUNCI:

Ya dace ace mun Ambato wasu daga cikin shubuhohi wanda ake kawosu game da hakkikin mata a musulunci a dai dai wannan gababar da muke magana akan mace, wanda wannan shubuhohi ana fadin su ke domin suka ga musulunci da kuma toshe wannan sura tashi me kyau da haske wanda ya kiyaye darajar da matsayi da girma da kuma kamalar mace tun lokacin bayyanar sa.

Lallai shubuhohin da suke yawo game da hakkokin mace a musulunci ta hanyar aiki tukuru wajen yin tarukan karama juna sani da kuma wasu buku bukuwa wanda suke da namufa na boye wanda yayi nesa da ikirarin baiwa mata yanci kamar yadda suke ikirari, amma bansani ba me yasa basa magana akan hakkokin yara da wanda aka zalumta da wanda aka kora aiki da masu rauni daga cikin maza da mata wanda aka zalumta cikin addinin su da rayuwan su cikin ko ina a fadin duniya a rika yin tarukan karawa juna sani da tarurruka akan haka wanda za'a nemi daga masu zubar da jinin mutane da su basu hakkokin su wanda suka kwace masu, sannan kuma me yasa basa kawo irin wannan shubuhohin sai a bangaren da suke ganin mummuna ne cikin tunanin wanda basu sani ba da duniya game da hakikanin addinin musulunci basa taba duba banagaren haske na wannan addini, a takaice daga cikin abubuwan da suke hanan hakan sune:

  • Shagaltar da hankulan mutane musulmi da wand aba musulmi ba daga abunda suke kullawa da kitsawa daga wurin mutane masu kare maslahar kansu da hadafi nasu wanda daga cikin maslahar su ce shagaltar da al'umma da kuma aiwatar da ikonsu da kuma karantarwan su zuwa ga abubuwa wanda suke sawwarawa akan cewa abubuwa ne muhimmai dukda cewa sun bar abubuwa wanda suka fi su muhimmanci, mu a matsayin musulmai munyi imani da cewa abubuwa ne anda basu kamata a yayata su saboda musulunci ya rufe su ya kuma yi bayanin su, suna fitowa ne a matsayin masu nasiha da binciken game da gaskiya masu hare hakkokin mace domin su janye hankalinta sannan daga baya su mayar da ita kamar dutse suna jifa da ita inda suke so sannan kuma su sanyata ta zama abinci ga wanda suke so su farauto ku janye su.
  • Son yada barna da munanan dabi'u cikin al'umma saboda duk al'ummar da munanan dabi'u suka yadu acikinta zasuyi sukin mulka da kuma amfani da arzikin kasar su a alherin domin maslahar makiyar su wanda suke kwadayin haka saboda duk mutumin da ya kasance burinsa cire kudi domin biyan bukatunsa da holewa da abubuwan da aka haramta zakaga baya iya bin dokar kasa ko kuma tsantseni wurin dukiyar sa, farfesa Henry Makow yana cewa[126]: lallai yakin kasashen turawa akan al'ummar larabawa da musulmai ya takaitu ne akan siyasa da wayewa da dabi'u, saboda burinsu shine harin dukiyan mutane bayan kwace masu abubuwan su masu tsada: addinin su da arzikin su na wayewa da dabi'u da kuma fitar da tsiraicin mata da lalata su.

Lallai himmatuwa da mace idan dai dagaske sukeyi kamata yayi su nema mata hakkokinta idan ta tsufa, idan ba haka ba ina kiransu da sukeyi na abata yancinta a matsayin ta na uwa bayan ta tsufa a lokacin da take neman taimako da kulawa, mu sani cewa musulunci yana kula da kyautata mata a wannan lokaci a matsayin neman kusanci zuwa ga Allah wannan shine abunda ake gani wanda yake yaduwa na gazawa cikin gidajen masu shelan neman yancin mace da kuma kare mata hakkoki, akwai abunda yafi kyawu game da hakkoki da kyautatawa da mutum zai bata wanda yake neman ladan haka a wurin Allah madaukaki kuma yana me neman yardan Allah da kusancin sa da tsoron azabar sa idan ya gaza wurin bata hakkokinta irin wanda sai da karfin doka ne kawai zai iya kwatan mata wanda idan doka ya bace hakkokin nata ya salwanta kenan, kuma ina mamakin irin wannan mujallar da suke yada hotunan mata masu kyau kadai banda munanan ko kuma tsofaffi, ko su ba matan bane? Ko kuma daman farauta ce da tallar haja ta

  • Keta da hassada daga wurin masu tsatsauran addinai na daban wand aba musulunci ba, sumo'il zuwaimar shugaban kungiyar taimako na taron karawa juna sani na kudus wanda akayi a shekara 1935, yana cewa[127]: lallai akwai muhimmancin bishara wanda muke koyar da kasashen kiristoci akwai domin su tashi akansa cikin kasashen muhammadiyya bawai kawai shigar da musulmai cikin addinin kiristanci bane domin kuwa a cikin haka akwi shiriya a garesu da karramawa, abunda muke so shine mu fitar da musulmi daga addinin musulunci… domin ya zama bawa wanda bashi da wani alaka da Allah.. daganan kuma sai ya zama bashi da wani alaka da dabi'u wanda al'umma suke dogaro akan sa wurin rayuwa.. saboda hakan aikin naku zai kasance ne a saukake cikin samun nasarar mulkan kasashen musulunci.

Wani kuma yana cewa: " idan muka samu daman fitar da mace ko kuma mu mallaketa to zamu kai ga abunda muke fata….. babu abunda suke fata face yada barna da munanan dabi'u ta hanyar mulkin mallaka da bautar da mutane, lallai sun kasance da abunda suke yadawa na wannan shubuhohi sunason bata musulunci ne da asalinsa, wannan wannan kiyayyar da keta baa ganin sa sai akan musulunci kadai da musulmai, lallai Allah yayi gaskiya cikin fadin sa cewa: " yahidawa da kiristocin bazasu taba yarda dakai ba har sai kabi addinin su, kace masu lallai shiriya itace shiriyar Allah kuma idan kabiyema son zuciyar sa bayan abunda yazo maka na ilimi baka da wani mataimaki ko majibincin al'amuran ka a wurin Allah (120)"[128]

  • Lallai munafar yada wannan shubuhohi game da hakkokin mace cikin musulunci tun wannan lokaci har zuwa yanzu shine fitar da mace daga cikin kamewarta da karamarta da janta zuwa ga munanan dabi'u da hatasta hakan, hakan kuwa yana faruwa ne ta hanyar sanya mace baturiya ta koma itace abun koyi wanda za'a rika kallo ana koyi da ita, kuma duk wata mace wacce ta karanta wannan littafi ta tambayi hankalinta musulma ce ko kuma ba musulma ba cewa shin halin da mace baturiya takai a cikin wannan zamani namu hali ne na martaba da daraja ga jinsin mace ko kuma hali ne na bakin ciki da tuzanci?, farfesa Hnry Makow yana cewa[129]: lallai budurwan America tana rayuna na hauka saboda mazaje da yawa suna saninta gabanin tayi aure sai ta rasa budurcinta wanda wani bangare ne na dandanonta ta koma daskararriya me makirci kuma wacce bazata iya soyayya ba, lalai mace a cikin al'ummar America tana samun kanta a matsayin jagora zuwa ga rayuwan maza wannan shine abunda yake sanyata ta zama muguwa birkitacciya wacce bai dace ba ta zama matan aurekodai ya zama cewa kawai hadafin shine jin dadin biyan bukata bawai dan soyayya ba ko son zuriya, lallaiuwa itace kololuwa na ci gaban mutum itace matakin da zata nesanta daga nutsewa cikin sha'awa domin mu zama bayin Allah.. tarbiyya da rayuwa sabo wanda tsarin duniya sabo baya son mukai ga wannan mataki na shiriya sunfi son mu zama ja'irai mayun wata wurin biyan bukata su rika gabatar mana da hotuna na batsa a maimakon aure.

Lallai dukkanin me hankali zai riski cewa matukar ana amfani da mace matukar akwai kwai da kuma rayuwa irinta dabbobi yananan to lallai kofofin fasadi a bude yake, idan tayi amfani da kyawunta da kuma dabi'a rin ta dabba sai ta koma kamar dutse a hannu su mayar da ita kamar haja wacce ake siya da siyarwa ta kafafen yada labari na karantawa ne ko kuma na gani ne da saurara domin ta kasance abunda jin dadi da biyan bukata lallai wannan sun tuzarta mace kuma sun yaudari matan aure kuma sun cutar da al'umma sun sabama makwabta, wannan a hakika sune wanda suka keta hakkokin mace suka kwace mata yancinta suka kuma kaita zuwa ga kofofin halaka, ina me irin wannan hali yake ga maganar manzon Allah s.a.w da yake cewa: " ina maku wasiyya da kyautatawa mata da alheri".

Lallai halin da mace ta tsinci kanta a cikin cikin al'ummar turawa na yanci mara tsari sakamako ne ta koma masu na abun da coci suka tabbatar cikin zamanin tsakiya game da hakkin mace na mugunta za zalumci da kuma keta hakkokinta da wulakanta darajarta ta yar adam masu hadafi da mataccen zuciya sunyi amfani da wannan dama ya watsa wannan yanayi domin su mallaki al'umma tare da jagorancin addini domin su fitar da al'umma wacce tayi nesa daga dukkanin dabi'u da manufa na gari domin su samu saukin amfani dasu wurin abunda suke so, amma musulunci babu mugunta da zalumci da keta hakkokin mata a cikinsa hasali ma ya daidaita su da maza ne cikin komai sai dai cikin abubuwan da aka daukaka jinsin na miji dashi akan jinsin mata wannan daukaka kuma ya ginu ne akan banbancin jiki da hankali tsakanin namiji da mace babu wanda zayyi inkarin cewa jinsi ne guda biyu mabanbanta jinsin namiji da mace daukakawan ya ginu ne akan wannan asali.

Dakta G.Lebon yana cewa cikin littafin wayewar larabawa: idan munason ganin tasirin alkur;ani cikin rayuwan mace ya wajaba a agaremu mu mu kalli halinsu a lokacin da larabawa suka wulakanta su ya bayyana cikin abunda masana tarihi suke fadi cewa suna da alaka da yanuwansu na kasashen turawa na irin halin da suke ciki, lallai turawa sun koyo dokoki daga larabawa na faransawa da abunda ya kunsa ya girmama mace, musulunci ba irin kiristanci bane shine wanda ya daga darajar mace daga can kasa wanda suka kasance a cikinsa sabanin abunda suke kudurcewa, idan kuma da duba zuwa ga kiristoci na zamanin tsakiya zakaga basu ba mace wani kima ba idan kuma ka bude littattafai na tarihin wannan lokaci zaka ga abunda zai gusar maka da dukkanun shakka akan haka kuma zaka sani cewa mazan wannan lokaci sun kasance suna gallazawa mata gabanin kiristoci su koyo mu'amala me kyau daga larabawa.

Lallai dukkanin mutum me hankali da fidira ta daidai me lafiya da wanin sa ma bazai yard ace mutumcin sa da darajarsa bay a zma haja wanda zasu mutane zasu rika amfani dashi domin biyan bukatunsu na sha'awa ba kawai, haka kuma duk wata mace me hankali da fidira me lafiya bazata so ta zama haj aba abun siye da siyarwa ko kuma filawa ga dukkanin me son shakanta sannan ya hurgar da ita kamar yadda ake hurgar da riga tsoho, lallai karantar wan musulunci a bayyane yake da fasaha da dacewa da fidira da hankali wurin kiyaye mabiyansa wannan karantarwan wanda yake hade da imani na zuciya me son alheri ga al'umma, musulunci yana tarbiyyan mabiyan sa akan kamewa da tsarki da kuma son daukaka, kuma yana aiki domin karantarwa me kyau wacce ta ginu akan imanin mutum da cewa Allah yana ganin sa wacce ta hanyar haka ne da yardan Allah zai gyara dabi'un sa, wannan shahabin saurayi da yazo gun manzon Allah s.a.w yace ya manzon Allah: kamin izini nayi zina!!! Sai mutane sukayi masa ca suna masa tsawa suna cewa: kayi mana shiru, sai manzon Allah s.a.w yace masa matso nan kusa dani ka zauna sai yace masa: " shin zakaso ayi zina da mahaifiyar ka?" sai yace: a'a wallahi bazan so ba Allah ya sanya ni fansa agareka, sai yace masa: " to haka mutane ma bazasu so ba ayi da iyayen su", sai yace: " to zakaso ayi da yarinyar ka?" sai yace: a'a wallahi bazan so bay a manzon Allah Allah ya sanyani fansa a gareka, sai yace: " to haka mutane su ma bazasu so ayi da yaran sub a", sai yace: " to zaka so ayi da yar uwanka?" sai yace: a'a ya manzon Allah Allah ya sanyani fansa a gareka bazan so hakan ba wallahi, sai yace: " to haka su ma mutane bazasu so hakan ba, sai yace: " to zakaso ayi da babar ka?" sai yace: a'a ya manzon Allah Allah ya sanyani fansa a agareka bazan so hakan ba wallahi sai yace: " to haka mutane ma bazasu so hakan ba" sai yace: " to zaka so ayi da innar ka?" sai yace" a'a wallah ya manzon Allah bazan so hakan ba Allah ya sanyani fansa a gareka, sai yace: " to haka su ma mutane bazasu so hakan ba, sai ya daura hannun sa akan kirjin say ace: " ya Allah ka gafarta masa zunuban sa ka kuma tsarkake zuciyar ka kuma kare masa farjin sa" daganan wannan saurayi be sake jin yana sha'awar aikata hakan ba[130].

Daga cikin wannan shubuhohi wanda ake yadawa akwai:

 

 

 

Maganan akan kara aure:

Lallai kara aure shari'a ce ta ubangiji baya halatta ga wanda yayi imani da Allah da littattafansa yayi inkarin haka ko kuma musanta hakan, Karin aure a musulunci sunna ce kamar sauran addinai irin sa wanda suke gabanin sa bawai kawai addinin musukunci bane me haka a'a kamar yadda muka fada ne cewa shari'a ce tsohuwa wanda addinai suka sani kamar su attaura da injila, dayawa cikin annabawa amincin Allah ya tabbata a garesu gabanin aiko da manzon Allah s.a.w sun kasance suna Karin aure wanda babu iyaka, ga annabi Ibrahim nan amincin Allah ya tabbata a gareshi ya kasance yana da mata biyu da annabi yakubu amincin Allah ya tabbata a gareshi yana da mata hudu annabi sulaiman kuma amincin Allah ya kara tabbata a gareshi yanada matadayawa… da sauran su, kenan maganar Karin aure bawai sabuwar magana bace dama can akwai cikin zamanin da suka gabata.

A cikin attaura: asfar cikin tsohon alkawari cikin littafi me tsarki a wurin yahudawa yana cewa: mace tare yar uwanta kada tazaman mata me cutarwa da bayyana al'aurarta na rayuwa.

basu haramta Karin aure ba sai dai sun haramta auren mace da yar uwanta a tare.

Kamar yadda ake ambata cikin attaura cikin safar samwel yazo cewa annabi dawud amincin Allah ya tabbata a gareshi ya kasance yana auren mata dayawa bayan kuyangun sa, haka kuma yazo cikin safari muluk cewa annabi sulaiman amincin Allah ya tabbata a gareshi ya ksance yana da mata dari bakwai da kuma kuyangu dari uku.

A lokcin da aka aiko musa kuma amincin Allah ya tabbata a gareshi ya tabbatar da Karin aure ba tare da ya kayyeje ma namiji adadin matan da zai aura ba har lokacin da bani isra'il suka kayyade adadin da mutum zai iya aura a cikin baitul makdis, sai dai malaman bani isra'il a cikin su akwai wanda suka hana Karin aure kuma acikin su akwai wanda suka halasta haka saboda rashin lafiyar matan ko kuma idan bata haihuwa.

Injila: annabi Isa amincin Allah su tabbata a gareshi wanda yazo domin cika shari'ar musa amincin Allah ya tabbata a gareshi babu wani nassi ko daya daya zo cikin injiwa wanda yake haramta Karin aure.

Sarkin Ireland disar mayyit[131] ya kasance yanada mata biyu shima sarkin fardiryak na biyu ya kasance yana da mata biyu tare da yardan coci akan haka kenan haramtawa da halastawa baya cikin addinin kiristacin kawai yazo ne daga wurin malaman coci.

Wannan martin lusar bajamushe wanda ya assasa mazhabar albirustanat wanda ya kasance ya yarda da Karin aure baya hawan kawari da tsarin hukunce hukuncen shari'ar almasihi kuma yana kira akan haka cikin dukkanin wuraren taro yana fadin Karin aure fa[132]: ni'ima ce lallai Allah yayi izini da hakan ga mutanen tsohon alkawari a lokacin wata lalura amma almasihi wanda yake son koyi dasu ya halatta a gareshi ya aikata hakan duk lokacin da yake da yakinin cewa lalurar sa tayi kama da nasu lalurar, domin kuma Karin aure yafi saki cikin ko wani yanayi.

Lallai haramcin kara aure yazo ne daga wurin malaman coci sakamakon dokokin da suka kawo amma baya cikin dabi'ar kiristanci, cocin wannan zamanin karkashin jagoranin fafaroma itace ta haramta Karin aure misali:

  1. Mazhabar arsoziksi baya halastawa daga daga cikin ma'aurata daya aure wanimiji ko mata daban matukar auren su yananan.
  2. Mazhabar arman arsoziksi kuma baya halasta daura wanin auren kuma na biyu sai bayan warware auren farko.
  3. Mazhabar ruma arsoziksi yana daukan aure wanda yake ci amatsayin abunda yake haramta wani sabon aure.

Larabawa a cikin zamanin jahiliyya: Karin aure ya kasance abu sananne a tsakanin kabilun larabawa a lokacin jahiliyya gabanin zuwan musulunci batare da iyakancewa bay a kasance namiji yana auren adadin matan da yake so.

Hakika Karin aure ya kasance sanannen abu tun zamanin da a wurin misrawa da farisa da siriyawa da japanawa da hindusawa kamar yadda yadda rusiya suma suka sani da kabilun jarmaniyawa kuma wasu daga cikin sarakunan girka sunyi aiki dashi.

Daga cikin haka zai bayyana cewa Karin aure bawai sabon abu bane wanda musulunci yazo dashi hakika al'ummomi gabanin zuwan muslunci sunsan haka kuma suna aikatawa, a lokacin da musulunci yazo sai ya halasta shi amma kuma ya sanya masa sharudda da dokoki na asali:

  1. Kada ya wuce mata hudu, saboda hadisin gailan dan salimata alsakafi wanda ya musulunta yanada mata goma sai manzon Allah s.a.w yace masa: " ka zabi hudu a cikin su"[133].
  2. Yin adalci da daidai to, tunda Allah ya halasta Karin aure sai ya sanya daga cikin sharadin haka yin adalci da daidaito da kuma rashin zalumci da rashin adalci a tsakanin matan. Manzon Allah s.a.w yace: " idan wani daga cikin ku yana da mata biyu kuma baya adalci a tsakanin su zaizo ranan alkiyama gefen jikin sa daya ya sanya"[134].

Abunda ake nufi da adalci da daidaito ashine cikin abunda ya shafi kudi da ciyarwa da kyauta da kuma rabon kwana amma abunda ya shafi soyayyar zuciya da jin son wata yafi na wata wannan babu lafi akan sa saboda abune wanda mutum bashi da iko dashi amma da kamar yadda Aisha tabada labarin haka Allah ya kara mata yarda tace: " manzon Allah s.a.w ya kasance yana raba kwana tsakanin matan sa da adalci, sa'annan yace: ya Allah wannan shine rabona cikin abunda nake da iko dashi, kada ka kama ni da abunda banda iko dashi kaine kake da iko akansa"[135].

  1. Iko da halin ciyar da mata ta biyun da yaranta. Idan ya kasance yanada sanin cewa bazai iya ciyar da mata ta biyun ba da yaranta ko lallai baya halatta a gareshi cikin wannan yanayi da ya kara aure.

Bari mu Ambato wasu daga cikin abubuwa wanda mafiya aksarin al'umma basa rabuwa dasu cikin al'ummomi sa'annan mu gani bayan haka cewa Karin aure maslaha ne ko kuma barna ne ga al'umma sannan kuma shin hakan maslaha ce ga mace ko kuma barna agareta?!

  1. Samun mace mara haihuwa kuma mijin yanason yara to cikin wannan hali menene yafi kyau da dacewa da wannan mata? Shin mijinta ya kara aure ta zauna a matsayin matar sa ko kuma ya saketa ba tare da wani laifi ba domin miji yana da hakki kamar yadda itama take da hakki na neman zuriya.
  2. Idan mace ta samu rashin lafiya na shanyewan wani bangare na jiki wanda bazata iya gudanar da ikinta ba na matan aure shin menen yafi anan wurin ga matar? Mijin ya kara mata aure ya kiyaye mutuncinta ko kuma ya sake ta ko kuma ya fita ya samo kawayen banza a waje?
  3. Wasu daga cikin maza sunada lafiya wanda mace daya bazata isheshi ba, ko kuma lokacin al'adarta ya zama yana da yawa, ko kuma wata rashin lafiya wacce sanadiyyar sa bazata iya gamsar da mijinta ba menene yafi anan wurin ga wannan mata? Shin mijin ya kara aure ko kuma yaje ya iya wannan bukata tashi ta hanyar haram?
  4. Cikin abunda babu shakka akan su cewa yawan yaki da matsaloli na cikin gida cikin mafiya yawan al'ummomi yana kasancewa dalilin kisan mazaje dayawa da barin mata mafi alherin dalila akan haka shine yakin duniya na daya dana biyu wand aka rasa sama da mutum miliyan ashirin na maza idan da ko wani namiji zai takaita ga auren mace daya to ina makomar sauran matan shin za'a tilastasu neman hanyoyin haram ne na biyan bukatar su..!! ko kuma zasu biya bukatar su ne ta hanyar shari'a wanda ya lamunce masu mutumcin su da karamar su ya kuma kiyaye masu hakkokin su kuma su haifi yara na halal ta hanyar yarda da Karin aure? Babau shakka cewa samun mata dayawa ba tare da aure ba zai sanya namiji fadawa hanyar alfasha.
  5. Samun zaurawa da mata marasa aure wanda suka manyanta to me yafi dacewa da mace cikin wannan yanayi? Ta zauna babu aure ko kuma rayuwa karkashin namiji wanda zai kiyaye mata karamarta da kuma kamewar ta tare da wata matan a karkashin sa.

Shin Karin aure akwaishi cikin wannan al'umma ta wannan zamani:

            Lallai Karin aure akwaishi cikin al'ummar wannan zamani sai dai cikin al'ummar da ba musulmai ba yana faruwa ne da sunan kawaye da yan uwa maimakon da sunan matan aure kuma wannan Karin auren yana kasancewa ne bada wani iyaka ba.. ko kuma wata siffa da doka. Haka kuma ba'a wajabta ma mijin daukan wani nauyi na wannan mata wanda yake zamantakewa dasu kawai idan ya biya masu bukata shinekan ya kuma bata mutuncin wanda ya hadu da ita da barinta da wahalar ciki da binsa.. haka kuma ba'a wajabta masa yarda da cewa wannan yaran nashi ne wanda aka samesu a wannan haduwar. Amma ta hanyar Karin aure a cikin al'ummar musulunci akwai iyaka da mata hudu kacal, sannan kuma yana kasancewa ne da daurin aure na shari'a, wanda yake wajabtawa mijin biyan sadaki ga mace, sannan kuma yaran da za'a samu ta hanyar wannan saduwar dole ne ya yarda cewa nashi ne a matsayin yaran shari'a suke a gunsa sannan kuma dole ne ya dauke nauyin ciyar dasu.

Meyuwa me tambaya zai iya tambaya cewaidan mun halasta Karin aure ga maza to me yasa suma mata bazamu halasta masu hakan ba?

Amsar itace neman daidaitawa tsakanin maza da mata cikin al'amarin Karin aure abune wanda bazai taba yiwuwa ba ta fidirar mutum da dabi'ar sa:

Rashin yiwuwar sa ta fidira: kasancewar namiji a fadin duniya cikin dukkanin al'umma yana da hakki na shugabantan gida saboda kasancewar sa yafi karfi mu kawar da ido akan wannanqa'idar na cewa wasu daga cikin mata sunfi maza karfi, idan ya kasance mace tana da maza biyu ko kuma sama da hakan to waye zai zama shugaban wannan gida? Sannan kuma wa zata yima biyayya da aiko wurin tabbatar da abunda suke so? Idan gam azan duka ne wannan bazai taba yiwuwa ba saboda kowa acikin su yanada abunda yake so saboda haka wannan zai bata masu rai!

Ta fuskar dabi'a kuma: dabi'ar mace shine bata daukan ciki sai sau daya a shekara kuma da namiji daya sabanin namiji wanda zai iya yuwuwa ya samu yara dayawa ta wuraren matan sa a lokaci daya, sannan kuma da za'a halasta Karin aure ga mace to da wani mijin ne za'a danganta wannan yaro?

Neman wasu daga cikin masu tunani na turawa da karin aure:

ya kamata mu ambaci wasu daga cikin maganganu na mutane masu tunani cikin turawa wanda suke neman Karin aure sannan kuma suna shi kadai ne hanya daya tilo na magance matsalolin al'ummar su.

  •  Dan falsafa me suna justaf lubon yana cewa cikin littafin sa me suna wayewan larabawa: lallai Karin aure yana nesantar da al'umma daga annobi da hadura kawance tsakanin miji da mata da kuma samun yara marasa ubanni watan tsintattu.
  • Mrs Annie Besant tana cewa cikin littafinta me suna addinan da suka yadu cikin indiya[136]: lallai ina karantawa cikin tsohon alkawari ( Attaura) cewa abokin Allah wanda yake tafiyar da zuciyar sa karkashin son Allah ya kasance yana Karin aure, Karin akan haka lllai sabon alkawari (injila) baya haramta karin aure sai ga bawa kawai ko kuma fada, wannan mutane biyun su kadai ne kawai aka wajabta masu zama da mace daya, kuma har wayau naga Karin aure cikin littafin hindiyya tsoho, ba komai yasa suke ake hutumar musulunci ba akan haka face ya kasance yanayima mutum sauki na bibiyan aibin addinin da ba nashi ba ya kuma shahara da hakan idan bah aka taya zai dace ga turawa suta yin gangami akan Karin aure wanda yake da iyaka a wurin mutanen gabas bayan karuwai sun yawaita a garuruwan su? Duk wanda yabi duddigi zai ga cewa kira da takaita aure ga mace daya ba'a girmama shi sai dai agun mutane yan kadan masu tsarki, baya halatta ace ma al'ummar basu yarda da Karin aure ba matukar akwai yaudara ga matan da suke aure na shari'a suna yin kawaye ba ta bayan gida, duk lokacin da muka auna al'amura da ma'auni na adalci zai bayyanan mana cewa Karin aure a musulunci wanda yake kiyayewa da ciyarwa da tufatar da mata ya rinjaye karuwan turawa wanda aka halasta masu namiji na dauke mace domin biyan bukatar sa kawai, daganan yayi hurgi da ita akan hanya bayan y agama biyan bukatar sa da ita, sun bayyana cewa dukkanin wannan al'amari abun kyama ne![137] sai dai baya halatta ga kirista ya zargi dan uwansa musulmi akan abunda sukayi tarayya acikin sa.

 

 

 

Shahadar mace:

Allah madaukaki yace: " kuyi sheda da mutum biyu cikin majazen ku idan kuma baku samu maza biyu ba to sai kuyi sheda da namiji daya da mace biyu cikin wanda kuka yarda da shaidar su saboda idan daya ta manta acikinsu sai dayan ta tuna mata"[138]

Allah madaukaki yayi bayani cikin wannan aya me girma cewa sheda wurin tabbatar da hakkoki bata cika sai da shedar maza biyu ko kuma namiji daya da mace biyu.

Kuma hakika hikmar Allah ya sanya mace ta zama tana da tausayi da rauni da kuma saurin karkata wanda hakan shine siffa na halin mace saboda taji dadin aikin dabi'ar ta na wannan rayuwa wanda ya shafi daukan cikin da shayarwa da reno wanda hakan yake bukatar zuciya me tausayi da rauni.

Asalin dabi'ar ta tana da tausayi wanda yake sanyata saurin jin tausayawa wanda hakan zai iya tasiri ga abunda take gani wanda kuma yake kewaye da rigan sheda wanda adalcin Allah ya nisantar da shedar ta cikin abunda ya shafi kisa da sauran shari'a ta ramuwa saboda zuwan irin wurin da zai iya karkarewa da kisa ko hukunci na ramuwa wanda mafiya yawan lokuta bazata iya jurewa hakan ba ko dai ta gudu ko kuma ta rufe idonta saboda kada taga abunda zai faru hakan ya faru ne saboda dabi'ar ta kamar yadda mukayi ishara akai wanda zai iyayin tasiri akan shedar ta.

Dukda cewa musulunci ya halastawa mace sarrafa dukiya ya basu hakki daidai da maza sai dai yanayin halittar mace sakon zamanta kewa na kwarai yana wajabtawa mata zama a gidajensu saboda gudanar da ayyukan sun wanda ya shafi iyali wanda yawanci macece me iya gudanar da hakan, hakan zai sanya mace tayi nisa da wuraren siya da siyarwa wanda mafiya yawanci fada yake faruwa a wurin da rikici na kudi koda kuwa mace ha halarci irin wuraren nan to zakaga yan kadan ne, kuma irin fadan da rikicin dake faruwa a wuraren sau dayawa mantawa takeyi bazata iya bada sheda ba akan haka idan an nemi shedar ta, sabanin idan su biyu ne mata a wurin da wannan abun ya faru zakaga mantuwan ko kuma kuskure babu shi kuma dalilin daya sa akace mace biyu ne zasu ba da sheda yawanci yazo cikin ayar cikin fadin Allah madaukaki: " saboda idan daya ta manta sai dayar ta tuna mata"

Watan tsoron kada dayar su tayi kuskure ko kuma ta manta sai dayan ta tuna mata wannan duka yana faruwa cikin al'amarin bawai kamar yadda wasu suke tunani bane cewa hakan yana cikin rage darajar mace bane da wulakantata domin kuwa da ace abun haka ne da ba'a amshi shedarta ba ita kadai cikin al'amuran daya shafi mata wanda maza basu sani ba sai mata. Ana amsar shedar mace ita kadai ba tare da namiji ba wurin tabbatar da budurcin mace da tabbatar da haihuwa da sauran aibin jiki da bakamantan su yayin kuma da ba'a amsan shedar namiji shi kadai koda kuwa cikin kananan abubuwa ne na dukiya zamu iya cewa mace ta kebanta dana muji wurin bada sheda ita kadai cikin abubuwan da sukafi hatsari akan kudi, almari ne wanda hukunce ke tabbata akansa.

Kamar yadda namiji ba'a amsar shedar sa shi kadai cikin al'amuran kudi dole ne sai da wani namiji kuma daban kafin a tabbatar da wannan hakkin amma babu wani wanda yace karfafa shedar namiji da wani dan uwansa namiji wukanta maza ne da kuma rage masu daraja.

Sannan kuma kari ga haka shine itafa bada sheda ba wani hakki bane wanda mutane suke rigegeniya akai a'a abune me nauyi wanda mutane ke gudun sa saboda haka ne Allah madaukaki yayi umurni da rashin gudu wurin bada sheda cikin fadin sa cewa: " kuma kada mutum yaki bada sheda idan an neme shi da hakan"

Wannan magana ta kunshi namiji da mace idan muka sani cewa sheda abuce me nauyi wanda mutane ke gudun sa saboda abunda yake cikinsa na cutar wa da kuma halartan zaman kotu wanda zai iya tsawaita da wahalhalun dake cikin haka na gajiya da kashe kudi kasancewar musulunci yana neman saukakewa mace abubuwa masu wahala na rayuwa wanda zai iya ko kuma ma ya dauke mata wasu daga cikin dukkanin wahalhalu kamar jagorantan gida da kuma ciyarwa lallai wannan girmamawa ne ga mace bawai wukantata bane.

Karin akan haka shune musulunci ya sansa shedar mace kalubantar shedar namiji dayin daidai dashi wurin bata shedar sa na tsinuwa a yayin da ya zargeta da zina kuma bashi da wani hujja akan haka, Allah madaukaki yace: " wanda suke jifan matayen su da zina kuma basu da sheda bayan su to shedar su shine mutum yayi rantsuwa da Allah sau hudu akan cewa gaskiya yake fadi (6) sai yacika dana biyar da cewa tsinuwar Allah ta tabbata a kansa idan dai karya yake mata (7) ita kuma abunda zai dauke mata azaba akan haka shine tayi rantsuwa da Allah sau hudu da cewa karya yake mata (8) sai ta cika da na biyar cewa fushin Allah ya tabbata akanta idan gaskiya ya fada (9)"[139].

 

 

Daukan nauyin gida da shugabantar sa:

Allah madaukaki yace: " maza sune masu tsayawa akan mata da shugabantar su saboda abunda Allah ya daukaka sashin su dashi akan sashi da kuma abunda suka kasance suna ciyarwa daga cikin dukinsu"[140].

Tsayuwa ana nufin shugabantar abu kuma hakan na maza ne banda mata saboda yanayin halittan namiji da hankalinta sifface wanda yake basu daman shugabantar gida, wannan wani al'amari ne na fidira kuma wata baiwa ce dalilin abunda Allah ya wajabtawa maza na tsauwaya da hakkin mace na ciyar da ita da kuma daukan nauyin rayuwanta na kiyaye ta da kula da ita da kuma lamunce mata abubuwan da take bukata na rayuwa namiji shune me kiwon gidanshi kuma za'a tambaye shi aka kiwon da aka bashi kamar yadda manzon Allah s.a.w ya fada hakan.

Ita mace ta fuskar halittanta na jiki tana da rauni saboda wasu abubuwa da suke samunta dayawa kamar su al'ada da ciki da haihuwa da shayarwa da reno wanda mafi yawancin lokato bazata iya tsayawa ba da shugabancin gida akan fuskan ta kamala.

Shi al'ada: yanada tasiri na hankali da bata ma mace rai kuma yana raunata jikinta saboda abunda take fitarwa a jikinta na jini a ko wani wata.

Ciki: mace tana rashin lafiya da yawa a lokacin sa, ko dai ciwon jiki saboda girman jarira acikinta da kuma tatsanta dayakeyi na baincinta sai ya sanya ta mata gajiya da kuma rashin karfin jiki wanda yake mata tasiri, ko kuma ta fuskar hankali saboda tsoron da takeyi ma dan cikin nata ko kuma kwallafa rai akansa da kuma tsoron abunda zai sameta a lokacin haihuwar ta wanda hakan yake da tasiri mammuna akan hankalinta kuma wuni lokaci kaga yayi tasiri akan mu'amalarta da harkokinta.

Haihuwa da abunda ke bayan sa: da abunda yake cikinsa na wahala da tsananin zafi wanda hakan yakeson ta samu hutu ba tare da yawan aiki ba ko kuma gajiyar da kanta na tsawon lokaci ya danganta da yanayin mace.

Shayarwa: lallai shayarwar mace ga jaririrnta yana sanya wani bangare na abincin da takeci ya tafi zuwa ga jaririnta wannan babu shakka yana da tasiri akan lafiyar ta yadda zakaga wasu mata a lakacin shayarwan su gashin kansu yana zubewa ko kuma kalarta ya canza ko kuma ta rikajin jiri.

Reno: renon jariri da abunda ya kunsa na bada lokaci da tsaya akansa domin kula dashi babu shakka yana daukan lokaci me yawa cikin lokutan mace.

Aqqad yana cewa[141]: lalai mace tanada halitta na tausayi na musamman ba irin na maza ba saboda yawan zaman da takeyi da jarirai wanda yake bukata abubuwa daya wanda zai dace dashi nayi masa wasa da kuma fahimtar sa da ita, da kuma yanayin ginuwar jikinta da kuma tausayinta da nashi haka shine asalin zuciyar mace wanda yasa take da saurin karyewa da tausayi sai kaga abunda yake ma namiji sauki yanayi mata wahala na hukuncin hankali da kuma rinjayin ra'ayi.

Kamar yadda dakta (Alexis Keyril) yake cewa wanda ya samu kayutar noble yana me bayyana banbanci gabbai tsakanin namiji da mace da cewa[142]: lallai abubuwan da suke banbanta mace dana miji bawai yana kasance wa bane kawai akan banbanci na gabbai na jiki da mahaifa da daukan ciki, kuma lallai bazata iyaba saboda sabanin hanyoyi na fahimtar ta, hasalima wannan banbancin a karon kansa dabi'a ce ta asali, na banbantan yanayin gudanar rayuwan jikin mace dana miji kamar yadda mace take banbanta dana miji ta wurin kimiyya na sinadari wanda yake tabbatar da rayuwan wani abu cikin mahaifarta, wanda suke kira da daidaito tsakanin namiji da jinsi me rauni basusan wannan banbancin ba na asali, suna kiran cewa dole ne ya zama sunada abu iri daya ta fuskar karatu da ayyuka da nauyi sai dai kuma mace a fili ta banbanta dana miji kacokan, ko wani bangare a jikinta yan akunshe da dabi'a na mace, haka kuma wurin gina gabobinta yasa banban dana miji kai hatta yanayin tsarin rauwan ta.

Kamar kuma yadda gabban namiji yafi karfi akan gabbai mace wanda wannan abu ne wanda kowa yake gani saboda haka maza suna aiki ne me wahala da gajiya wanda mace bazata iya ba cikin mafiya lokuta dogaro ga abunda ya gabata zai bayyana cewa cancantan namiji na shugabantan gida da tsayuwa akan mace.

 

 

Hakkin mace cikin gado:

Musulunci yazo yabawa mace hakkinta cikin gado bayan ta kaance bata da hakkin cikinsa, kenan gado ya kasance hakki ne na maza wanda suke kare kabila suke kuma tsareta daga abokan gaba, al'amarin bai tsaya ba kawai akan haka ya zama cewa itam gadonta a keci Kaman kama, yazo daga Ibn Abbas Allah ya kara masu yarda yace cikin fadin Allah madaukaki: " yaku wanda sukayi imani baya halatta a gareku da ku rika gadon mata ta dole, kuma kada ku hanasu tafiya da wasu daga cikin abubuwan da kuka basu" sai yace: sun kasance idan namiji ya mutu yan uwansa su sukafi cancanta da matar sa idan sun so su aureta idan kuma sun so su aurar da ita ga wanda suke so su suka cancanta da ita akan iyayenta sai wannan aya ta sauka akan haka[143] .

Sai musulunci yazo ya haramta hakan, Allah madaukaki yana cewa: " yaku wanda sukayi imani baya halatta a gareku da ku rika gadon mata ta dole, kuma kada ku hanasu tafiya da wasu daga cikin abubuwan da kuka basu"[144].

sai ya bata hakkinta cikin gado ya kuma wajabta mata kaso na wajibi, Allah madaukaki yana cewa: " maza suna da kaso cikin abunda iyaye suka bari ko kuma yan uwa haka mata suna da kaso cikin abunda iyaye suka bari ko kuma yan uwa kadan ne ko kuma dayawa, kaso ne wanda yake na wajibi (7)"[145].

Sayyid kudub Allah ya masa rahama yana cewa cikin tafsirin wannan aya[146]: wannan shine tsari na farko wanda ya wanda musulunci y aba mata tun karni na gima sha hudu hakkin gado kamar maza, kamar kuma yadda ya kiyaye hakkoki kanan wanda a lokacin jahiliyya suke zalumtarsu su cinye masu hakkokin su, domin zamanin halihiyya sun kasance suna kallon irin aikin mutum a yaki da kuma samar da wani na noma ko kuma kasuwanci, shi kuma musulunci yazo ne da manhaji na ubangiji wanda yake kallon mutum a karon farko a darajarsa ta mutum wannan itace daraja ta asali wanda bata barin sa cikin ko wani hali sannan kuma ya kalli mutum gwargwadon daukan nauyin sa cikin na waki'in wanda ya shafi iyalai da waki'in jama'ar sa.

Allah maduakaki yana cewa: " Allah yana maku wasiyya cikin yaran kun, namiji yanada rabo irin na yara mata biyu"[147]

Zai iya zuwa kwakwalwan wanda be fahimci hikimar musulunci ba akan haka idan ya karanta wannan aya da cewa ya toye hakkin mace inba haka bay a zaice mace tana da rabin kason namiji cikin gado?!

Allah madaukaki yayi bayani dalla dala na gadon mace ya kuma sanya gadonta cikin yanayi guda uku:

  • Wani lokacin kasonta a gado daidai yake da kason namiji.
  • Wani lokaci kasonta a gado dai dai yake da kason na miji ko kuma kasa da haka.
  • Wani lokaci kuma kasonta a gado rabin kason na miji ne wanda wannan shi yafi yawa.
  1.  Me son Karin bayani akan wannan maudu'I sai ya koma zuwa ga littattafan ilimin gado wanda sukayi bayani dalla dalla kuma cikakke akan haka.

Gabanin muyi hukunci akan musulunci da cewa shinny a toye hakkin mace cikin gado ko kuma be toye mat aba bari mu dauki misali akan haka wanda zai bayyana mana hikimar da yasa aka ba mace rabin kaso na gadon namiji: mutum yam utu ya bar yaro namiji da yarinya mace ya bar kudi a misali dubu uku na riyal, kason namiji a ciki zai zama dubu biyu idan an raba ita kuma mace dubu daya.

Bari mu duba mugani bayan wannan rabo halin namijin da mace yadda zai kasance bayan wani lokaci, ta bangaren na miji wannan kudin daya gada zai ragu saboda za'a nemi ya biya sadaki ga matar da zai aura sannan kuma ya shirya gidan da zasu zauna da daukan nauyin dukkanin abunda suke bukata na wannan gida da kuma daukan nauyin rashin lafiyar duk wanda bashi da lafiya cikin wannan gida da kashe kudi akan matar da yaranta da biya masu bukatar su wanda ba'a daurawa matan hakan ba da cewa ta daukai wani bangare na ciyar da gida koda kuwa ta kasance me kudi ce, kamar yadda har wayau shidai aka daurawa nauyin ciyar da iyayen sa da yan uwansa wanda ya zama wajibi ya ciyar dasu idan sun kasance talakawa ko kuma sun tsufa shi kuma yana da halin haka.

Ita kuma macen an karramata da daukakata bugu da kari da soyayya da kuma kula da ita da ciyarwa ba tare da an daura mata daukan wani nauyi ba na kudi kuma ba'a daura mata kashe kudi ba hatta akanta, kenan kudin data gada zai karu ba raguwa zayyi ba saboda zata amshi sadaki daga mijinta lokacin da zai aureta koda kuwa sun rabu mijin dai shi ne zai dauki nauyi ciyar da yaranshi da bukatunsu, zata iya jujjuya dukiyar ta ta hanyar kasuwanci ko kuma makamancin haka da sauran hanyoyi na habaka dukiya.

Zai bayyanar baya cikin abunda ya gabata cewa rabon mace zai kasance tanaji a gareta a halin da iyalenta suka rasa ta, shi kuma na kuma namiji abun da ya amsa zai karar dashi ne wurin ciyarwa daboda abubuwan da aka daura masa na nauyi. Lallai shari'ar musulunci ta banbanta da auran dokoki da tsari na duniya wanda uba yake barranta daga yarinyar sa idan takai wasu shekaru a rayuwa ta yadda dole ta fita nemo ma kanta loman abinci domin ta rayu ta hanyoyi daban daban, yarinya a musulunci wajibi ne daukan nauyinta a musulunci har sai tayi aure daganan kuma daukan nauyinta ya koma kan mijinta daganan kuma ya koma kan yaranta.

Lallai tsarin da suke daidaita mace dana miji wurin gado sai su daidaita ttsakanin su wurin daukan nauyi da wahalhalu na kashe kudi dai dai da daidai. Amma neman ba mace kaso irin na namiji ba tare da neman daidaita sub a wurin ciyarwa da daukan nauyin kudi babu adalci a haka lallai hakan akwai zalumci ga maza irin wanda shari'ar musulunci baya yarda dashi.

Kenan daga cikin adalci shine a wurin daukaka namiji akan mace cikin gado ya dauke mata nauyi na kashe kudi wanda ya kunshi ciyarwa na gida da yara da makamantan su, hasalima muna ganin saukin musulunci da karramawar sag a mace a lokacin daya yafe mata dukkanin wajibi na kudi ya daurama namiji kuma dukda haka be hanata gado bay a bata rabin kason dayaba na miji shin hakan baya cikin adalci?

Abunda ya dace a rika shelansa shine kowa cikin maza da mata yanada kaso cikin gado wanda babu wanda ya isa ya hana shi wannan kaso nashi saboda haka ne musulunci ya iyakance wasiyyan da mutum zai iyayi da dukiyar sa a lokacin mutuwar sa da sulusi zuwa kasa da haka babu wata hanya na haramtawa yara gadon abunda mahaifin su ya bari ko kuma cutar dasu, an karbo hadisi daga Amir dan sa'ad dan Abi waqqas daga babanshi Allah yakara masa yarda yace: manzon Allah s.a.w ya ziyarce ni a lokacin hajjin bankwana bayan ciwo yakaimun makura sai yace masa: hakika wannan ciwo yakai mun makura kuma ni mutum ne me arziki kuma babu wanda zai gajeni sai yarinya guda daya tilo zan iya sadaka da biyu cikin uku na kudi na? sai manzon Allah s.a.w yace masa: " a'a" sai nace: to rabi ba? Sai yace: " a'a" sai nace: to sulusi fa sai yace: " sulusi sulusi ai yanada yawa lallai kabar magadanka masu arziki shi yafi ka barsu mabukata suna dogara da mutane lallai bazaka ciyar da wani abu ba kana neman yardan Allah da hakan ba face an baka lada akan sa hatta lomar da zaka sanya cikin bakin matar ka"[148].

Sai manzon Allah me daraja s.a.w ya kiyaye hakkokon mace karkashin karantarwan sa da umurnin sa wanda zai samar mata da rayuwa me karamci.

Kari akan haka kuma cewa dukkinin kudin diyyar da yan uwan mutum zasu biya da duk abunda ya shafi ukuba na kudi maza ne kawai suke biya banda mata.

 

 

Diyya:

A cikin shari'ar musulunci diyyar mac rabin diyyar na miji ne hakan kuwa yana faruwa ne cikin yanayi guda daya na kisa bisa kuskure wanda aka wajabta biyan diyya akan sa bekai matakin kisasi ba, amma a halin kisan da gangan wanda sakamakon sa shine kashe wanda yayi kisan idan yan uwanda wanda aka kashe basu yafe ba to a wannan hali hukuncin mace dana miji daya babu banbanci shin me kisan namiji ko mace sannan wanda aka kashe din namiji ne ko mace cekasan cewar su dukkanin su mutane ne.

Amma hakin kisan kuskure kuwa wanda ake biyan diyya wata kila kasancewar diyyar mace rabin diyyar namiji hakan zai koma ne zuwa ga gwargwadon cutarwan da zai shafi iyalan wanda aka kashe. Iyalen da aka kashe masu baba bisa kuskure wanda shine me kula da al'amuran su da ciyar dasu da daukan nauyin su akan bukatuwar su lallai rashi ne ta fuskar dukiya wanda ya kunshi talauci da kariya da reno ta fuskar ma'ana kuma ya kunshi tausayi da rangwame sai dai tausayin sa da rangwamen sa bekai na mahaifiya ba.

Shi kuma iyalin da aka kashe masu mahaifiya bisa kuskure suna rasa uwa ce ta fuskar ma'ana kawai wanda ya kunshi tausayi da lallashi da reno da sauran abubuwan da suka shafi mace wanda cikin mafiya lokuta maza basa iyawa wannan fuskar kuma da za'a biya kudin duniya duka bazasu iya zama makwafin haka ba.

Ita diyya bawai biyan darajar wannan mutumi da aka kashe akeyi ba kawai ana kiyasta cutarwan da zai shafi wannan iyali ne, idan muka sani cewa wannan cutarwan da zai shafi wannan iyali saboda rashin baba ko kuma uwa zai bayyanan mana bangare cikin bangarorin da yasa diyyar mace ya zama rabin na namiji.

 

 

Aikin mace:

Lallai Allah madaukaki ya halicci mutum mace dana miji ya kuma sanya soyayya da tausayi a tsakanin su abunda zai sanya taimako atsakanin su na raya duniya. Kamar yadda Allah madaukaki ya kebance namiji da karfi da kuma iko na daukan nauyi abunda yake sanyashi fita fadin kasa neman kudi haka Allah ya kebance mace da yanayin aikinta kamar ciki da haihuwa da shayarwa da reno da abunda ya kebanci haka na tausayi da rahama da lallashi dogaro akan wannan halitta ta Allah zai kasance abunda yafi dacewa da namiji a dabi'ance itace aiki a wajen gida, ita kuma mace aiki acikin gida.

Lallai musulunci be hana mace aiki ba hasalima ya halasta mata kulla cinika da kuma juya dukiyarta dayin kasuwanci da siye da siyarwa ya kuma sanya hakan ya zama ingantacce ba tare da yardan mijin ba ko kuma mahaifinta. Sai dai kuma ya sanya dokoki da kuma kayyade hakan da tsari da sharudda ta yadda idan aka rasa daya daga cikin wannan dokoki ko sharuddda zai tashi taga halacci ya koma haramci, daga cikin wannan sharudda akwai:

  1. Dole ne ya zama cewa babu cin karo tsakanin aikin mace da kuma aikinta na gida ta yadda aikin nata bazai zama sababi ba na rashin cika hakkokin mijinta da yaranta wanda yake kanta ba ko kuma kuma shafe sa idonta ba a cikin harkokin gida, sabod amace a cikin musulunci kamar yadda muka ambata a baya tanada hakkokin ta akan mijinta haka shima yanada hakkokin sa kanta haka suma yaranta sunada hakkoki akanta, manzon Allah s.a.w yana cewa: "mace me kiwo ce a gidan mijinta kuma za'a tambaye ta akan kiwonta…."[149]
  2.  Aikinta ya kasance tare da mata yan uwanta wanda babu cakuduwa da maza da gogayya dasu hakan saboda kiyayeta da kuma nesantata daga abunda zai iya zama sababi na ribatanta da kuma fada mata daketa mutuncinta da karamarta daga wurin wasu mutane masa imani, manzon Allah s.a. yana cewa: " dayan ku baya kebanta da wata mace face shedan ya kasance na ukun su"[150].

Wata marubuciya ta turanci me suna (lady koke) tana cewa cikin jaridar eco:[151] lallai cudanya yana maza suke hadashi, saboda haka ne mace take son yin abunda zai sabawa fidirarta, kuma gwargwadon yawan cakuduwa tsakanin maza da mata gwargwadon yawaitan yaran zina wannan bala'i ne me girma.

Sayyid kudub Allah yayi masa rahama yana cewa[152]: lallai yana daga cikin hakkin maza kamar yadda yake daga cikin hakkin mata su samu natsuwa zuwa ga abokan su kuma kada wani yak eta mutuncin wani wanda zai iya canza tausayin wani akan abokinsa idan hakan be kai ga canza barna da kura kure bai wanda hakan ke zama kalubale da hadin kai da wayewa da kuma natsuwa, wannan canzawan da ayyukan dake faruwa na barna a kullum cikin al'umma wanda akwai cakuduwa a cikin su sannan kuma mace take fita cikinsu cikin ado kuma shedanun fita da rudan mutane su fito tare da ita, wannan magana ce wanda bashi da kima wanda yanayi yake karyata wa abunda harsunan mabarnata suke furtawa da masu sharri cewa cakuduwa tsakanin maza da mata yana rage sha'awa sannan kuma yana sanya ko wani jinsin sanin ladubba na magana da kuma ladubba na zamanta kewa, yana kuma karawa mutum fikira na kiyaye kai daga kaskanci kuma zabin abokin aure ya danganta ne akan gwaji cikakke hatta kura kuran da suke ciki yana zama lamuni ne ga cewa mutum zai iya rike abokin zamansa saboda shi ya zabeshi da yardan sa bayan gwaji, zance wannan yana rusa abunda yake faruwa aka, domin kuwa abunda yake faruwa na canji cikin zukatan mutane da kuma lallata gidaje da saki da rashin saki da yaduwar yaudara na aure yana aukuwa cikin wannan al'umma. Maganar su na cewa hakan yana rage sha'awar mutum da kuma yanayin haduwa da iya magana sai su tambayi yara yan makarantan sakandire na mata a America wanda yawansu yakai kasha 48 cikin dari a daya daga cikin makaruntu su, shi kuma nasaran gina gidan aure bayan wannan cakuduwan d zabi sais u tambayi yawan gidajen da saki ya daidaita cikin America kuma hakan yana karuwa lokaci bayan lokaci kamar yadda cakuduwa ke karuwa da kuma zabin.

  1. Aikin mace ya kasance a tun asalinsa halal ne kuma ya dace da dabi'ar mace, kada mace tayi aiki cikin abunda da ya sabawa dabi'arta kamar aiki na kamfani me wahala da aikin yaki da aikin da akwai wulakantata aciki kamar aikin tsabta wanda ya kebanta da maza kawai da share hanya cikin abunda da shari'a bata yarda dashi ba ga mace a musulunci.

sai dai a wannan gabar tambaya zai zo mana cewa me yasa mace take aiki?

Idan tana aiki ne domin ta rayu ta ciyar da kanta to hakika musulunci ya kiyaye mata wannan hakkin saboda tsarin ciyarwa a musulunci dole ne akan uba daya ciyar da yarinyar sa har sai tayi aure idan tayi aure kuma ciyarwanta da yaranta ya koma kan mijinta idan mijin nata kuma yam utu ciyarwanta ya dawo kan mahaifinta idan bata da mahaifi kuma ya koma kan yaronta idan yaran nata kanana ne to dolene yan uwanta sa dauki nauyin ciyar da ita haka dai wajabcin yake kan wanda yafi kusa da ita, ita mace tun daga haihuwarta har zuwa mutuwar ta bata da bukatar sai tayi aiki kafin zataci abinci domin ta rayu duka anyi mata haka domin ta zauna tayi aikinta na zaman takewa wanda ake mata hassada akai wanda wannan aiki nata ya shafe aikin gida da tarbiyyan yara na kwarai wanda baya bukatar wani karfi da wahala me yawa wanda zai iya daukan lokacinta dayawa da tunaninta.

Wani malami na turanci yana cewa: samuwell samayelse yana cikin manya jigon na turanci[153]: lallai doka da tsarin daya ke yake ba mace aiki cikin bangaren arzikin kasa koya yake to lallai sakamakon haka ruguza rayuwan mace ne na gida, saboda hakan yaci karo da taswiran gida, ya kuma rusa rukunan iyali, ya kuma jijjiga hadin kan al'umma, domin kuwa yana kwace mace daga mijinta da yaranta da yan uwanta, ya zama da wani nau'i na daban wanda bashi da wani sakamako sai na gusar da kyawawan dabi'un mace, saboda aikin mace na hakika shine tsayawa akan aikin gidanta misali na kimtsa gida da tarbiyyan yara da kula da arzikin da hanyoyin rayuwanta tare da tsayawa akan bukatu na gida, sai dai mace me aiki ya hanata aikata dukkanin wannan wajibobi ta yadda gidaje suka koma Kaman ba gidaje ba, yara kuma suna tasowa babu tarbiyya, ya ajiyeta a lungun kasala, ya kashe mata son na mata, ya kuma fitar da mace daga kasancewar ta matan aure abokiya masoyiya ga namiji ta koma abokiyar aiki da wahala, tana kwana da wasu tasiri wanda cikin mafiya lokuta yana share mata Kankan yanayinta na tunani da kuma dabi'u wanda suke taimakawa wurin kiyaye falalar ta.

 

 

Kasancewar saki a hannun maza kawai banda mata:

Saki ya kasance a zamanin jahiliyya beda wani tsari, miji zai iya sakin matar yadda yaso ya kuma dawo da ita yarda yake so, sai musulunci yazo da tsari da dokoki domin kiyaye mace daga zalumci da zunubi da wasa da sakin yake faruwa akanta, hakika mutane sun kasance a zamanin jahiliyya miji yana sakin matar sa yadda yake so kuma ita matar shi ce idan ya dawo da ita cikin iddarta, koda kuwa zai saketa ne sau dari ko kuma sama da haka, har mutum zai ce ma matar shi: wallahi bazan sakeki ba wanda bazan iya dawowa dake ba wani namijin ya aure ki sannan kuma bazan kara daukan nauyin ki ba da ciyar dake har Abadan, sai tace yah aka to ke nufi: sai yace: zai sake ki duk lokacin da iddarki ta kusa karewa sai na dawo dake, sai alkur'ani yasauka yana cewa: " saki sau biyu ne, ko dai ka riketa da kyautatawa ko kuma ka rabu da ita da kyautata"

Hakaki musulunci ya sanya saki ya zama halal domin bukata da lalura wanda rayuwa bazata iya tafiya ba dashi.

Kuma shari'a musulunci tana kokorin ta samo mafita tun farko na warware sabanin da ya kunno kai tsakanin miji da mata saboda kada ayi saki, Allah madaukaki yace: " idan mace taji tsoron zagi da cutarwa da kawar dakai daga mijinta babu laifi a garesu da suyi sulhu a tsakanin su, kuma yin sulhu shi yafi zama alheri"[154]

Me yasa saki ya zama a hannun na miji? Yanayi na dabi'a da hankali shine cewa saki ya kasance a hannun namiji ba mace ba saboda abubuwan da aka daura masa na kashe kudi akan matar da kuma gida, matukar dai shine wanda yake biyan sadaki da kuma samar da wurin zama da daukan nauyin ciyar da ita lallai ya kasance hakkin sa ne ya daukan hukunci na karkare wannan rayuwa na aure ya zama a hannun sa matukar dai yana shirye akan daukan asarar kudi da kuma na hankali wanda zai samu baya saki saboda ya sani cewa fa lallai sakin nan zai kawo masa asara na kudi da kuma rasa sadakin sa wanda ya biya da sannan kuma idan zai sake wani auren sai fa ya kashe irin wannan kudi wanda yayi asarar su.

Kari akan haka kuma shine har wayau na miji cikin mafiya galibin lokuta yana iya hadiye fushin sa da kuma samun iko akan abunda zai faru a lokacin sabani da fada a tsakanin ma'aurata. Sau dayawa namiji baya komawa zuwa ga saki sai a mataki na karshe idan komai yaci tura na ci gaban zaman wannan aure.

Dukda haka musulunci bata hanawa mace neman saki ba daga wurin miji mace tana da hakkin saki ya kasance a hannunta idan an sharada hakan a lokacin daurin auren kuma mijin ya yarda da hakan.

Saboda shari'ar musulunci shari'a ce wacce ta dace da fidira saboda haka tana riskan hakikani zuciyar mutum da abunda yake kai komo a cikinta na ji da tausayi kamar yadda yaba namiji hajjin rabuwa da matar sa idan yaji bayasonta daya saketa, haka yaba mace wannan hakki idan taji batason zama dashi saboda yana munana mata zamanta kewa ko kuma fada mata maganganu marasa dadi ko kuma duka ko kuma yana da wani aibu na halitta kamar ya kasance me karamin azzakari ko kuma baya iya jima'i ko kuma batajin sha'awarsa ko kuma yaki saduwa da matar ko wani rashin yafiya ya sameshi me hatsari bayan aure ko dai makatantan haka tana da hakkin neman a raba aure sai dai wannan ana kiransa da suna daban watan "kul'i" shine bace ta biya mijinta abunda ya bata na sadaki da kuma abunda ya kashe a lokacin aure wanda sukayi ittafi akai wannan shine karshin adalci saboda cewa itace takeson raba wannan aure, koda kuwa mijin yaki aiwatar da wanann kul'i tana da damar zuwa wurin alkali ko kuma shugaba ya bata hakkinta.

Rashin daidaita mace dana miji wurin amsar aure:

Lallai aikin zabin namijin aure wanda ya dace ga mace al'amari ne wanda akai wahala aciki wanda wahalar sa yafi yahalar namiji ya zabi matar da ta dace dashi saboda idan ya aure mace wacce bata dace ba dashi yana da daman canza ta cikin sauki.. amma ita mace kamar yadda muka fadi a baya tana da rauni cikin al'umma saboda haka ne musulunci ya himmatu da kareta da kuma yi mata rigakafi daga dukkanin wani abu mara kyau ya kuma yi umurni da rashin gaggawa wurin zabin miji wanda na dace da ita saboda mace kada ta zama ragon yanka a gun mijin wanda akarshe itace zata fi cutuwa saboda haka ne musulunci ya sanya sharudda na ingancin aure wanda shine waliyyi ko kuma wanda zai wakilce sa wanda aure baya kulluwa sai dashi saboda fadin manzon Allah s.a.w cewa: " babu aure sai da waliyya da kuma shedu guda biyu adilai, duk auren daya kasance ba da hakan ba to batacce ne, idan sunyi sabani shugaba shine waliyyin wanda bashi da waliyyi"[155].

Kamar yadda musulunci ya sanya daga cikin ingancin aure samun waliyyi haka kuma yasanya amsar wannan mata ga miji da kuma izininta ga waliyyanta shima sharadi ne na ingancin aure, idan aka tilastawa mace akan aure tana da hakkin daukaka kara zuwa ga alkali domin ya raba wannan aure saboda hadisin alkansa'u diyar juzam tace: mahaifinta ya aurar da ita tana bazawara bataso sai taje gun manzon Allah s.a.w ta fada masa "sai ya warware aure"[156].

Dalilin kasancewar waliyyi sharadi na ingancin aure shine kasancewar sa cikin mafiya lokuta yana kwadayin ganin maslahar yarinyar sa, duk wanda yayi ikirarin cewa cikin wannan al'amari a kwai toye ma mace yancinta na zabin wanda takeso ta yarda da ya zama mijinta sai ace masa: lallai muuslunci yaba mace me hankali balagaggiya budurwa ce ko kuma bazawara hakkin yarda ko kuma rashin yarda da wanda aka gabatar mata ta aura kuma ba'a yarda ba ga waliyyinta daya tilasta mata ko kuma aikata wani abunda zai tilasta mata yarda da wanda bataso saboda fadin manzon Allah s.a.w cewa: " kada a aurar da bazawara har sai da izininta sannan kuma kada a aurar da budurwa har sai an sanar da ita ta amince sai sukace ya manzon Allah ya zamu gane amincewar ta sai yace idan tayi shiru"[157].

Lallai shari'ar musulunci lokacin da tayi kira gayin aure bawai hadafinta biyan bukata bace kawai da haka na dan wani lokaci a rabu a'a yana da hadafin kulla alaka ce me daurewa, lokacin daya kasance mace itace dayan bangaren na wannan alakar sai ya wajabta yardanta da amincewar ta da hakan.

Sai dai kasancewar mace me rauni a dabi'ance wanda take da suarin tasirantuwa da abubuwan da suke kewaye da ita wanda zasu sanyata biye ma zahiri sai musulunci ya shar'anta wa waliyyinta amsa ko kuma kin amincewa da wanda yazo neman aurenta wanda be dace da itaba saboda namiji yafi sanin mace sanin halin namiji saboda kasancewar su jinsi iridaya, amma idan miji wanda ya dace yazo kuma macen ta yarda dashi shi kuma waliyyinta yaki yarda dashi bada wani dalili ba sai kawai iko da mallaka to an dauke walitakarta akansa an mayar dashi wurin dan uwanta makusanci idan bata da yan uwa sai alkali ya aurar da ita.

Lallai musulunci ya hana mace auran namiji mara kamewa kuma wanda be dace ba da ita da kuma iyalanta saboda mace da iyalinta za'a rika aibatasu da miji mara kamewa sannan kuma kaskanci zai same su ta dalilin sa, auren mace ga namijin ta waliyyinta da yan uwanta basu yarda dashi ba hakan zai zama dalili na yanke zumunci wanda Allah yayi umurni da sadar dashi, kuma ma'aunin hakika na miji nagari shine abunda da hadin manzon Allah s.a.w ya nuna: " idan wanda kuka yarda da addinin sa da dabi'un sa yazo neman aure agunku to ku aura masa idan kuma ba haka ba fitina da fasadi me girma zai bayyana a doron kasa"[158].

Saboda mijin da yake da addini da dabi'u na gari idan yanason matar sa zai girmamata idan kuma baya sonta bazai wulakantata ba da kaskantar da ita zaiji tsoron Allah a game da ita.

 

 

Tafiyar mace ba tare da muharrami ba:

Lallai mace a musulunci lulu-lulu ce wanda ake bata tsaro da kuma zinari me dajara wanda ba'a yarda aji mataba ko kuma a tabata ba sai da ga wanda yake da hakkin haka, musulunci yana rigakafi ne wanda yafi magani amfani shiyasa ya hana mace tayi tafiya ita kadai batare da muharrami ba kamar miji ko uba ko wani ko kani ko kuma wani dan uwa wanda ya haramta ta aura saboda fadin manzon Allah s.a.w cewa: " kada mace tayi tafiya ba tare da muharrami ba kuma kada wani namiji ya shiga wurinta face akwai muharrami a tare da ita" sai wani mutum yace ya manzon Allah s.a.w: ni inason na fita cikin sojojin yaki na kaza kuma matata tanason yin aikin haji ya zanyi? Sai yace masa: " yi maza kabi matar ka"[159].

Mutum zai iya cewa cikin wannan hanin akwai toye yancin mace da kuma take mata hakki! Saboda wannan shine abunda da zai zo cikin zuciya farko al'amari sai dai da munsan illar haka da dalilin wannan haramcin shubuhar da take tare damu zata kau kuma zai bayyanan mana cewa lallai wannan aikin fan a musulunci yayi ne saboda yana son kare darajar mace da kuma tsareta… bawai son wulakantata yake yi ba da takaita mata yancinta, sau dayawa tafiya akwai wahala a ciki da kashe kudi, ita kuma dabi'ar mace tana da rauni ta bangaren halittan jikinta saboda abubuwan da suke bijiro mata na lalura kamar yadda muka fada abaya na al'ada da ciki da shayarwa da kuma rauna ta zuciya wanda take da saurin jayuwa zuwa ga tausayinta da tasirantuwa da abubuwan da suke kewaye da ita wanda hakan ba aibu bane hakika manzon Allah s.a.w ya kira su da kwalabe kinaya ga zartsin su da raunin su, an karbo hadisi daga Anas dan malik Allah ya kara masa yarda yace: manzon Allah s.a.w ya ksance cikin wata tafiya tare dashi akwai wani yaro nashi baki wanda ake ce masa Anjashatu yana waka sai manzon Allah s.a.w yace masa ka rika tausaya ma (kwalabe) watan mata"[160]  

Mace a halin tafiyarta tana bukatar wanda zai zai kareta daga bata gari wanda zasuyi mata ta'addanci akan dukiyar ta ko kuma mutuncinta wanda bazata iya kare kanta ba game da haka cikin mafiya lokuta saboda raunin jikinta. Kamar yadda kuma take bukatan wanda zai dauke mata bukatunta a biya mata abunda take nema da yassare mata harkokinta, muharrami ga mace a musulunci ana neman aikata dukkanin wannan ayyuka daga wurin sa ta yadda bazata nemi taimakon wani mutum ba bare, a takaice muharramin mace me hidima ne a gareta da gadi domin kareta daga duk wani wanda zai iya fada mata cikin ashararen mutane, to ina wulakanta mace yake anan wurin?

Lallai hakan mutuntu mace ne da daukaka a gareta, ta samu wanda zayyi kishi akanta ka kare karamanta, ya kuma kiyayeta daga wargin masu wargi da mata hidima da biya mata bukatunta da abunda take nema.

 

 

 

Haramcin dukan mata a musulunci

* Ahmad Al-Amir da Tsekoura Vivian

 

Gabatarwa

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya aiko Muhammad me bushara da gargadi da kuma kira zuwa ga Allah da izinin sa da fitila me haskakawa, ya kuma daukaka sahabban say a basu falala me girma, amincin Allah me tarin yawa a jere ya tabbata a kan Muhammad da iyalan sa da sahabbansa baki daya.

Bayan haka na rubuta wannan littafi ne a matsayin raddi akan shubuhohi ga wanda shedan ya rude su ya kuma batar dasu bata me girma, hakika nayi magana akan matsalar dukan mace a musulunci a wurare da dama kuma muna gani a yanar gizo wanda suke bada fatawa ba tare da ilimi ba akan wannan al'amari sannan kuma makiya musulunci sun jibge akan wannan al'amari suna masu kirkiran karya da shedar zur daga cikin maganganu wanda basu da tushe balle makama, saboda haka ne na naga ya dace na rubuta wani littafi ga makaranci na bayyan matsayar musulunci game da dukan mace da kuma banbancin sa da sauran addinai banbanci bayyananne, lallai shi kadai ne addinin da ya nassanta akan haramcin duka mata yarinya ce ko kuma babba ce, ga bayanin gareku sannan bayan haka sai kuyi hukunci akan al'amarin bayan karantawa da kuma ilimi akan haka.

                                                                        Mawallafi……

                                                                                    Ahmad Amir.

 

 

 

Babi na farko

Aikata ayyuka dai dai da shari'ar musulunci

Lallai dayawa daga cikin ayyukan mutane suna aikata su ne karkashin inuwar shari'a na musulunci karkashin hukunce hukunce masu zuwa a dunkule saboda hukuncin aikin ya bayyana a garemu tsakanin halasci ko kuma haramci:

  1. Farilla: wannan shine kololuwa wurin martaba na ayyukan bayi, shine duk wani abu da Allah ya nema aikata shi wanda yake dole da wani dalili kai tsaye wanda babu shubuha a cikin sa, kamar umurni da yin salla da azumi da karatun alkur'ani, hukuncin sa shine lazumtar aikata haka da kuma zuwa da abunda aka bukata daga bawa na wannan ayyuka tare da samun lada akan aikatashi ko kuma zunubi akan wanda yaki aikatashi.
  2. Mustahabbi: shine dukkanin abunda Allah yayi umurni dashi ba akan fuskar dole ba, ana bayar da lada ga wanda ya aikata shi sannan kuma babu zunubi ga wanda be aikatashi ba, kamar misalign asiwaki kafin fara salla.
  3. Halal: shine dukkanin abunda babu lada akan aikatashi ko kuma zunubi akan barin shi, kamar tafiya da hawan mota da makamantan su na dukkanin abunda aka yarda da aikatashi cikin ayyuka na al'ada na rayuwan mutum na yau da kullum.
  4. Makaruhi: shine dukkanin abunda Allah ya hana hana aikatashi ba akan dole ba, ana bada lada ga wanda yabar aikatashi domin biyayya ga Allah kuma babu zunubi ga wanda ya aikata shi, sai dai anason ya nesanta daga gareshi da kuma abunda ya kunsa sai dai baza'a rubuta zunubi bag a wanda ya aikata shi, sai dai yawan maimatashi da dogewa akan shi zai iya sa mutum ke tare iyakokin Allah da kuma fadawa zuwa ga abunda Allah mabuwayi da daukaka ya hana aikatawa, dalilin da yasa baza'a rubuta zunubi ba ga mutumin daya aikata makaruhi dukda cewa aiki ne wanda aka kyamace shi saboda zai iya yayi ne domin biyan wanin lalura me girma da yanayi na rayuwan mutum wanda zai sanya shi aikata wannan aiki da yake makaruhi, misali ubangiji madaukaki yana kin saki amma be haramta shi ba akan bayin sa domin fadada masu al'amuran su idan akwai laluran aikata hakan.
  5. Haramun: shine dukkanin wani aiki da Allah ya hana aikatashi a fuskar wajibi da wani dalili kai tsaye wanda babu wani shubuha a cikin sa, ana bayar da zunubi ga wanda ya aikata shi sannan kuma akwai lada ga wanda yabar aikata shi domin biyayya ga Allah, Kaman haramcin shan giya.

 

Banbanci tsakanin halal da haramun:

Lallai sanin halal da kuma banbanta shi daga haram shine ginshiki na musulunci da kuma dalili akan imani, yana hade ne da ayyukan zuciya kamar yadda kuma yake hade da ayyukan gabbai, hukuncin asali na aikata abubuwa shine halal babu haramun sai ga abunda dalili yazo ingantacce kuma a bayyane akan haramcin sa, haramtawa da halastawa hakki ne na Allah madaukaki, kasancewar sa shine mahalicci da reno da saukakewa da bada ni'ima yana halastawa bayin sa abunda yake so ya kuma haramta musu abunda yake so, sai dai saboda rahamar Allah madaukaki da falalar daga gareshi ya sanya halal da haram domin dalilai wanda ake iya hankalta wanda yake komawa ga maslahar mutum, akan wannan Allah madaukaki be halasta wani abu ba face me dadi kuma be haramta komai ba sai datti.

Canzawar aiki daga wannan gida na hukunci zuwa wani gida:

  1.  canzawar aiki daga halal ya koma gidan haramci ko kuma akasin haka:

aiki na halal zai iya canzawa zuwa haramun idan aka samu dalilai wanda zasu say a canza maimakon aiki ya zama me kyau wanda rai ke sonsa zuwa aikin mummuna wanda yake cutar da jiki, misali akan haka shine hukuncin sharia na yawo akan hanya shine halal, sai dai zai iya canzawa zuwa haramun idan wani shugaba na musulunci na wani kasa ya karrara haramcin yawo daga karfe goma na dare misali akan wasu tutuka ko kuma cikin wasu bira ne saboda wasu dalilai na tsaro wanda zai iya kaiwa ga rasa ran mutum.

                        Aiki na haramun zai iya canzawa zuwa halal idan aka samu dalilai wanda zai sanyashi haka na lalura domin kiyaye rai daga halaka, kamar shan giya, shan giya hukuncin sa haramun ne sai zai iya zama halal idan mutum ya bata hanya acikin sahara ya kusan mutuwa saboda kishi kuma bai samu ruwa ba sai giya, a wannan yanayi zai sha giyan nan gwargwadon yadda zai kiyaye ran sa daga halaka amma kuma bazai wuce wannan kima ba.

  1.  Aiki ya canza daga wajabci zuwa haramci ko kuma akasin haka:

 Aikin zai iya canzawa daga wajabci zuwa haramci, kuma aikin na haramun zai iya canzawa zuwa na wajibi, saboda dalilai wanda zai kawo hakan kamar yadda mukayi bayani a baya, misali salla wajibi ne sai dai aikata salla zai iya zama haramun idan mutum yayi salla a cikin gidansa a tsakiyar girgizan kasa me tsanani wanda yana da tabbacin fa zai halaka idan dai be fita daga wannan gidan ba da sauri!! Ko kuma ta'addanci ga mutum na yanke masa kafa hakan haramun ne sai dai uziri na rashin lafiya zai iya a yankewa mutum kafar sa domin ceton rayuwan daga halaka to anan wurin yanke kafan wannan mara lafiya ya zama wajibi akan likita domin masa magani idan kuma be aikata hakan ba yana da laifi kuma Allah zai azabtar dashi akan rashin yanke wannan kafa ta mara lafiya.

  1. Canzawan aiki daga makaruhi zuwa zuwa mustahabbi, da kuma canzawan aiki daga mustahabbi ko kuma sunna suwa haramci:

Aiki na makaruhi zai iya canzawa zuwa mustahabbi ko kuma wajabci, misali saki aiki ne wanda yake makaruhi a shari'a Allah madaukaki yana kyamansa sai dai a wani lokutan rashin sakin matan zai iya kaiwa zuwa ga haramun wanda babu wani hanya da zai gusar da hakan sai sakinta, kamar idan mace ta kasance me karancin kamun kai kuma ya kasa gyarata anan wurin abunda yafi shine ya saketa, anan wurin aiki makaruhi ya zama mustahabbi.

Aiki mustahabbi zai iya komawa haramun, misali yin asuwaki aiki ne wanda yake mustahabbi amma zai iya zama makaruhiko kuma haramun idan hakoran mutum suna ciwo zasu fita ya kuma san cewa idan fa yayi asuwaki zasu fita, a cikin wannan hali yin asuwaki yaci karo da ka'ida ta shari'a cikin musulunci wacce tace (babu cuta kuma babu cutarwa).

 

A takaice:

A takaice da dunkule maganar da sharhin sa ya gabata shine muslunci ba addini bane makaho wanda baya gani kuma bay alula da uzirin mutane da ikon sun a rayuwa nay au da kullum, lallai makanci ya hakika yana cikin idanun makiyan sa ne wanda suke son yada shubuhohi da kararyaki akan musulunci domin su rufe hasken Allah kuma Allah sai ya cika hasken sa koda kuwa kafirai basaso.

                        Me yuwa ne yakai me karatu me karamci kasan cewa musulunci ba addini ne ban a zalumci addini ne na adalci, shi kuma adalci suna cikin sunayen Allah kyawawa, saboda haka haramci da halastawa a cikin musulunci sun ginu ne akan adalci ba akan makanta ba, shi kuma zalumci baki dayan sa haramun ne a cikin shari'ar musulunci.

 

Babi na biyu

Mu'amalantar matan aure a karkashin hasken alkur'ani da sunnar me tsarki

 A cikin hasken nassoshi na alkur'ani me girma Allah madaukaki yayi umurni da kyautatawa ga mata da kuma karramata da rayuwa da ita me dadi hatta bayan karewan soyayya ta zuciya, Allah madaukaki yace: " kuyi zama dasu me kyau da dadi, idan kun kyamaci su to wata kila fa kuna kyamatan abu sai Allah yasa masa alheri me yawa"

(suratun nisa'i ayata 19)

Kuma manzon Allah s.a.w yana cewa: " kada mumini ya kyamaci mumina idan ya kyamaci wani dabi'a daga gareta zai yarda da wasu". Muslim ne ya rawaito shi.

Allah madaukaki yayi bayanin hakkokin mata akan mijinta kamar yadda mijin shima yake da hakkoki akanta, sai Allah madaukaki yace: " suma sunada kwatankwacin abunda yake kansu na kyautatawa"

(suratul bakara ayata 228)

Wasiyyar manzon Allah s.a.w ta kasance gabanin rasuwar sa da kula da dama da karrama su da kuma rashin zalumtar su da danne masu hakkokin su, manzon Allah s.a.w yace: " ina maku wasiyya na alheri game da mata" muslim ne ya rawaito shi.

Ya kuma kara cewa s.a.w: " wanda yafi muminai cikan imani shine wanda yafisu kyawawan dabi'u kuma zababbun ku sune wanda suka kasance zababbu ga iyalan su" tirmizi da ibn hibban ne suka rawaito shi, tirmizi yace hadisi ne hasan sahih kuma yana cikin littafin sahihul jami'u lambar hadisi na: 1230.

An karbo hadisi kuma daga Aisha Allah ya kara mata yarda tace: manzon Allah s.a.w yace: " mafi alherin ku shine wanda ya zama mafi alheri ga iyalan sa kuma ni nafiku zama mafi alheri ga iyalai na". Ibn hibban ne ya rawaito shi cikin littafin san a sahihi da tirmizi hadisi na 3314 cikin littafin sahihul jami'u.

Ya kuma yi umurni da hakuri akan kura kuran su da kuma raunin hankalinta da kuma kawar dakai daga kaskancinta yana me bayyana dabi'ar mace wanda Allah madaukaki ya halicce ta akai, sai manzon Allah s.a.w yace: " lallai mace fa an halicce ta ne daga kashin hakarkari, bazata taba mike maka ba, idan zakaji dadi da ita kaji dadi da ita a haka a karkacenta, idan kuma kace zata mikar da ita zaka karya ta ne kawai, karyata shine sakinta". Muslim ne ya rawaito shi.

Ya kuma kara fadi har wayau cewa: " ina maku wasiyya na alheri ga mata saboda an halicce su ne daga kashin hakarkari kuma mafi karkacewar kashin hakar kari shine na sama, idan kace zaka mikar dashi zaka karya shi idan kuma ka kyale shi hakan zaici gaba da zama a karkatanshi, sabo da haka ina maku wasiyya na alheri akansu". Buhari ne ya rawaito shi.

 

Shin manzon Allah s.a.w ya taba dukan wata daga cikin matan sa ko sau daya ne?

Maznon Allah s.a.w shine abun koyin musulmai wanda Allah ya wajabta masu bin sunnar sa, Allah madaukaki yace: " hakika kunada koyi na kwarai daga manzon Allah ga wanda yake kwadayin samun rahamar Allah da rana ta karshe ya kuma ambaci Allah dayawa".

(Suratul ahazab ayata 21)

Shine abun kuyi na kololuwa da kuwa dabi'a masu daraja Allah ya aiko shi da addini mikakke kuma ubangijin sa ya tarbiyyantar dashi ya kuma kyautata tarbiyyan sai ya kasance abun kuyi wurin kyawawan dabi'u da halaye na gari, Allah madaukaki yace: " lallai kana kan dabi'u masu girma".

(Suratul kalam ayata 4)

Yayi aiki da kyawawan dabi'un sa a aikace akan abubuwan da suka faru ya sanyata kuma suka zama milali na gani, cikin fadin sa s.a.w: " an aiko ni ne domin na cika kyawawun halaye". Malik ya kawo shi cikin muwadda da kuma buhari cikin adabul mufrad kuma yana cikin littafin sahihah lambar hadisi na (45).

Matar sa Aisha tana fadi game dashi wacce tasan bubuwan shi mu'amala saba da sahabban sa: " dabi'un sa ya kasance alkur'ani ne". ahmad ne ya rawaito shi cikin sahihul jami'a(4811), watan yana bin umurnin da yayi yana kuma barin dukkanin abunda da ya hana babu wata dabi'a ta kwarai wanda alkur'ani ya kwataidar akanta face manzon Allah s.a.w ya kasance wanda yafi kowa riko da ita, kuma babu wata dabi'a mara kyau wanda alkur'ani ya hana face manzon Allah s.a.w ya kasance wanda yafi kowa tsananin nisantar sa.

 

Shin ya zo cikin tarihin sa cewa ya taba dukan wata mace ko kuma yaro ko sau daya ne?!!!!

Hakika duk wanda yake bibiyan tarihin sa da lura cikin hadisan sa masu daraja zai gani a bayyane cewa manzon Allah s.a.w ya hana hakan kuma ya tsawatar akan haka matuka, matar sa Aisha Allah ya kara mata yarda tana cewa game dashi: " manzon Allah s.a.w be taba dukan komai ba da hannun sa ko mace ko wani bawan sa me masa hidima sai dai yayi jihadi fisabilillah. Kuma ba'a taba masa wani laifi ba ya rama sai dai idan an keta hurumin Allah shine yake ramako domin Allah madaukaki mabuwayi" msulim ne ya rawaito hadisin [ ma'anar hadisin shine ba'a taba cutar dashi bay ace zai dau fansa ko kuma ramuwa ba sai dai idan an keta iyakokin Allah sai ya taimaki hakan ya kuma ladabta wanda ya keta su].

Kai hatta makiyan sa wanda suke kokarin bata da'awar sa da kuma katange mutane daga gareta basu taba tabbatar da wani abu akan haka ba wanda yake sabama abunda muka ambata.

Bari muka abunda wanda yafi kusanci dashi cikin mutane ya kuma lazimce shi sosai wanda babu shakka dadewa da lazimtar mutum zai bayyana maka halayen sa baki daya, hadimin sa Anas dan malik yana cewa game dashi wanda yayi masa hidima na tsawon shekaru goma:

" na yima manzon Allah s.a.w hidima na tsawon shekaru goma amma be taba cemun ba kul ko sau daya, kuma be taba cemun ba game da wani abu dana aikata me yasa ka aikata ko kuma abunda ban aikata ba yacemun me yasa baka aikata shi ba? Manzon Allah s.a.w ya kasance yafi kowa kyawawun dabi'u cikin mutane" muslim da tirmizi ne suka rawaito shi.

 

Babi na uku

Hukuncin miji ya duki matar sa a musulunci?

Lallai inda ake samu dalilai a musulunci shine cikin nassosi na littafin Allah madaukaki da sunnar manzon sa in gantacce me daraja amincin Allah ya tabbata a gareshi da sahabban sa da iyalan sa, daga cikin wannan abubuwa biyun ne zamu kafa hujja dasu wanda a karkashin su ne zai bayyanar mana hukuncin dukar mace a cikin musulunci shin hakan wajibi ne ko kuma mustahabbi ko halal ko makaruhi ne ko kuma haramun daga cikin hadisin da Iyas dan Abdullahi ya rawaito inda yace: manzon Allah s.a.w yace: " kada ku rika dukan bayin Allah mata, sai umar yazo wurin manzon Allah s.a.w yace masa: mata suna bijirewa mazajen su, sai yayi ramgwame akan dukan su sai gidan manzon Allah s.a.w ya cika da mata suna kawo koken mazajen su, sai manzon Allah s.a.w yace: " hakika gidan Muhammad fay a cikia da mata suna kokawa akan mazajen su to wa'innan basu basa cikin zababbun su". Abu dawud da ibn majjah da darimi ne suka rawaito shi, albani yace hadisi ne ingantacce.

A karkashin sharhin wannan hadisin me dajara zai abubuwa Kaman haka zasu bayyanan mana:

Lallai hadisin nan na manzon Allah me girma be fade shi ba a lokaci gudu kuma a zamani daya, ya fadeshi ne s.a.w cikin zamani guda uku mabanbanta:

Zamani na farko: manzon Allah s.a.w yace a cikinta " kada ku rika dukan bayin Allah mata" wannan shine karshen zamani na farko da wuri na farko.

A bisa da haka duk wanda yaji wannan maganar daga manzon Allah s.a.w zai sani cewa lallai hukuncin dukan mata a muslunci haramun saboda manzon Allah s.a.w ya hana kuma duk wanda ya aikata hakan ya sabama Allah kuma za'a hukunta shi saboda ya sabama wannan umurni na manzon Allah s.a.w.

Zamani na biyu: zuwan Umar dan kaddab Allah ya kara masa yarda a lokacin da ya sabawa lokacin farko wanda manzon Allah s.a.w yace acikin sa: " kada ku rika dukan bayin Allah mata" domin kawo kuka akan mata da cewar sa: mata suna bijirewa mazajen su. Watan ma'ana basa bin umurnin su kuma suna kausasa masu da magana kuma sun galabe mazajen su, anan ne manzon Allajh s.a.w yayi rangwame da dukan mata saboda amfani da yayi da ra'anin sa na fiqhun zamani da lalura na rayuwa wanda rayuwa bazayyiwu ba sai dashi, sai dai kuma yaye yanayin wannan duka yake? Wannan shine abunda zamuyi magana akan sa nan bada jimawa ba.

Zamani na uku: bayan izinin manzon Allah s.a.w ga, mazaje da kudan matan su wanda suke saba masu da bijirewa akan mazajen su, sai mata dayawa sukazo gun manzon Allah s.a. yana kokawa akan mazajen su, sai manzon Allah s.a.w yace: " hakika gidan Muhammadu ya cika da mata suna kokawa akan mazajen su lallai wannan mazajen basa cikin zababbun cikin ku"

Wannan shine zamani na karshe wanda hukuncin haramcin dukan mata ya bayyana a cikin musulunci wanda hakan makaruhi ne da kuma haramun idan mijin ya ketare iyakokin Allah -wanda zamuyi bayanin haka nan bada jimawa ba- shin za'a fahimta cikin wannan nassin hadisin cewa manzon Allah s.a.w ya kwadaita akan dukan mata? Ko kuma yayi shagube ne ga dukkanin me dukan matar sa? Lallai cikin maganar sa s.a.w akwai rashin mugunta da kuma kore alheri ga mutumin dake dukan matar sa?!!!

Hakika sahabbai Allah ya kara masu yarda sun fahimci isharar wannan maganar ta manzon Allah s.a.w kuma sun gane cewa lallai duk wanda yake dukan matar sa bazai taba samn yardan da kyautatawa ba daga manzon Allah s.a.w, babu shakka kuma cewa duk abunda manzon Allah s.a.w be yarda dashi ba to yana cikin hukuncin makaruhanci me tsanani wanda hakan zai iya kaiwa zuwa ga haramun.

Hasali ma a lokacin da mijin Fadima ditar kais ya saketa wasu mutum biyu sun zo sun nemi aurenta wanda sune mu'awiya dan abu sufyan da Abu jahmin da usama dan zaid Allah ya kara masu yarda, a lokacin ne manzon Allah s.a.w yace mata: " shi mu'awiya mutum ne talaka, shi kuma abu jahmin mutum ne me yawan dukan mata amma shi usama dan zaid" sai ta fada da hannun cewa: usama! Usama!". Muslim ne ya rawaito shi.

 

Shin dukan mace zai iya canzawa daga makaruhanci zuwa haramci?

Hakika mun gani yadda yake cewa asali da hukuncin farko akan dukan mata haramun ne sa'annan ya canza ya zama halal saboda wasu dalili da magani na musamman wanda suka sanya hakan daga nan kuma ya canza zuwa makaruhanci babba, sai dai yaushe ne dukan mace yake zama haramun? Dukan mace yana zama haramun ne idan ya kasance najin ciwo maimakon wanda zai ladabtar kawai ba tare da jin ciwo ba lallai dukkanin ta'adi cikin musulunci haramun ne idan ya kasance zalumci ne ko kuma muganta, Allah madaukaki yace cikin littafin sa me hikima yana tsawatarwa gane da dukkanin nau'in zalumci: " duk wanda yayi zalumci daga cikin ku zamu dandana masa azaba me girma"

(suratul furkan ayata 19)

Kuma manzon Allah s.a.w yana cewa: " kuji tsoron zalumci domin kuwa zalumci duhu ne ranar alkiyama" muslim ne ya rawaito shi.

An kuma karbo hadisi daga Anas Allah ya kara masa yarda yace: manzon Allah s.a.w yace: " kuji tsoron addu'ar wanda aka zalumta koda kuma kafiri ne saboda addu'ar sa bashi da wani shamaki tsakanin sa da Allah". Ahmad ne ya rawaito shi kuma albani ya inganta shi.

Musulunci ya haramta cutarwa koya yake da dukkanin surorin sa da nau'ukan sa shin na magana saboda fadin Allah madaukaki cewa: " lalllai wanda suke jifan mata muminai kamammu wanda babu ruwan su an tsine masu duniya da lahira kuma suna da azaba me girma".

(Suratun nur ayata 23)

Ko kuma cutarwa na jiki da kuda da makamantan sa sai idan ya kasance a bisa hakki ne, saboda fadin Allah madaukaki cewa: " wanda suke cutar da muminai maza da mat aba tare da wani laifi ba to haki sun daukan ma kansu nauyi da zunubi bayyananne"

(suratul ahazab ayata 58)

Wannan haramcin ya shafi kowa cikin mutane maza da mata kanana da manya musulmi da kafiri, an karbo hadisi daga abi huraira Allah ya kara masa yarda daga manzon Allah s.a.w yace: " musulumi shine wanda mutane suka kubuta daga sharrin harshen sa da hannun sa mumini kuma shine wanda mutane suka amince masa akan dukiyar su da jinin su". Sanunan al nisa'i, sheikh albani yace hadisi ne hasan sahih.

Duk wanda yace musulunci yana ta'addanci ko kuma mugunta ko dukan mace to hakika yayi kage ga addinin Allah karya me girma.

 

Hukuncin alkalanci na musulunci akan dukan mace:

Alkalanci ta musulunci yana daukan al'amarin dukan mace da cutar da ita daga wurin mijinta da matukar muuhimmanci sannan kuma beyi kasa a gwewa ba wurin hukunta ladabtarwa ga miji akan me ta'adi da zalumci da mugunta ba akanta kuma yana dabbaka shi a aikace da hukunci na shari'a a duk lokacin da aka kawo kara akan haka, misali wannan kararraki masu zuwa:

  1. Sharidar riyad ta yada akan shafinta na intanet a kwanan wata 12/12/2012 labari kamar haka:

Kotun koli akan laifuffuka na yankin jihar katif cikin kasar saudiyya tayi hukunci akan miji akan ta'addancin da yayi ma matar sa na duka da cewa za'ayi masa bulala 30 a idon mutane saboda haka ya zama izina ga masu ta'addanci akan matar su, sannan kuma tayi masa hukunci har wayau da zai karantar a daya daga cikin makaruntu na gaba da sakandire a fannin mu'amala tare da matan aure da kuma al'amarin iyali, sannan kuma zai gabatar da jarabawa na rubutu wanda zai sanya shi a cikin fayel din wannan shari'a.

Akan irin wannan matsala dukkanin kotuna cikin garuruwan musulmai baki daya suna hukunta miji wanda yayi ta'addanci ga matar sa da duka, ta dayan bangaren kuma matan da suke tsoratar da mazajen su da nuna su da makami ko kuma niyyar cutar dasu da makirci ga mazajen su ana masu hukuncin bulala ba dayawa ba daganan kuma akaisu wurin yan sanda domin wannan aiki nasu da sukayi ma mazajen su idan mijin ya barranta daga wannan tuhumar.

Abunda muke so a cikin wannan hukunci shine lallai musulmi me hankali wanda yake bin karantarwan musulunci baya yarda da zalumtar mace ko kuma yi mata ta'addanci, kamar yadda addinin mu ya be karantar damu ba ko kuma umurtan mu da hakan sai dai ya haramta mana hakan ya kuma sanya hakan cikin ayyukan zalumci na haramun, hasali ma ya umurce mu ne da hakuri da yafiya da kawar dakai da kuma sakayya akan laifi da kyakyawan aiki, dukda cewa musulunci be sanya dukan mace ya zama halal ba ya dai sanya shi ya zama a wasu lokutan kadai ya kamata ayi hakan idan ya rayuwan ma'aurata bazai gyaru ba sai dashikuma ya kayyade hakan da sharudda wanda zai sanya hakan ya zama yayi karanci sosai domin tabbatar da burin daya wanda shine kiyaye gida da kuma ladubban jama'a cikin al'umma baki daya.

 

Babi na hudu

Hukunce hukuncen musulunci a halin bijirewar mace

Mutum zai iya cewa shin baya fi dacewa ba da namiji ya rika yima matar sa wa'azi idan ta bijire maimakon dukanta, sai muce mas aba haka bane wannan shine hukuncin Allah madaukaki me buwaya wanda yace cikin littafin sa me hikima:

" Wanda kuma kuke tsoron bijirewar su kuyi masa wa'azi a farko sannan ku kaurace masu a wurin kwana sannan kuma ku duke su, idan kuma sunyi maku biyayya to kada kirkizo wani hanyar cutarwa a gare su, lallai Allah ya kasance madaukaki ne me girma".

(Suratun nisa'i ayata 34)

Manzon Allah s.a.w kuma yace cikin hajjin san a bankwana:

" ku saurara kuji ina maku wasiyya na alheri game da mata domin lallai suna rayuwa ne akarkashin ku amma baku mallaki komai ba da ya wuce haka game dasu, sai dai idan sunzo da alfasha bayyananne, idan suka aikata haka to ku kaurace masu a wurin kwana sannan kuma idan basu shiryu ba sai ku duke su duka bana jin rauni ba, idan kuma sukayi maku biyayya to kada ku kirkiro wata hanyar zalumci akan su. Ku saurara kuji lallai kuna da hakki akan matan ku haka suma suna da hakki akan ku" tirmizi ne ya rawaito shi, albani yace hadisi ne hasan.

Haka zamu rika ganin yadda Allah madaukaki me hikima yake bayyana mana cikin hikimar sa masani ga harkokin bayin sa da manzon sa me daraja hanya domin magance matsalolin mace wanda ta bijire a hankali har zuwa matakai uku:

  1. Mataki na farko:

Ya nuna ma miji hanyar wa'azi da nasiha a matsayin mafita na farko domin gyara macen da ta bijire kafen kaurace mata a wurin kwana wannan matakan wajibi ne binsu a jere a wurin mafiya yawan malaman fiqihu, ya wajaba akan namiji ya kusanci zuciyar matar sa da maganganu masu dadi da kuma jiyar da ita abunda zai lallashi zuciyar ta ya kuma nuna mata muhimmancin ta a wurinshi da cewa lallai yanasonta da alheri yana mata nasiha ya kuma aiwatar da ikon sa akan mata nasiha da wa'azi wurin ganin cewa ya gyara halinta, musani cewa fa wa'azi baya zuwa daga busashiyar zuciya ko kuma da usulubi mara kausasawasai dai yana samuwa ne da magana me dadi da kuma mu'amala kamar siyan kauta ga mace har ta amshi maganar mijinta da zuciya daya kuma cikin yarda,hakika ya wajaba akan mace me kwakwalwa da dabi'u kyawawa data wa'aztu daga maganar mijinta tana kallon makomar gidanta da yaranta, amma idan mace ta kasance me taurin kai me mummunan hali to nasiha baya amfanar da ita ko kuma wa'azi ko fadakarwa sai mijin ya aikata abunda zai iya cikin haka sai ya tafi zuwa mataki na biyu cikin jerin kamar yadda Allah madaukaki ya umurce mu dashi wanda shine kaurace mata a wurin kwana.

  1. Mataki na biyu:

Miji ya bi hanyar kwarace wa a wurin kwana watan ya juya mata baya kuma kada ya kusanceta har na tsawon kwana uku amma kuma kada ya wuce kwanaki uku saboda fadin manzon Allah s.a.w cewa: " baya halatta ga musulmi daya kaurace ma dan uwansa sama da kwana uku". Muwadda da buhari da buslim duk sun rawaito shi.

Domin ya tsawatar mata akan aikinta wannan shine mataki na biyu kuma damace ga matan domin ta gyara cikin wannan lokaci na tsawon kwanaki uku, idan ta gyara halinta to ya wajaba a gareshi dana yanke wannan kaura nashi ya yafe masa da nasiha idan kuma taci gaba dayin girman kai da dagawa ya zama wannan kauracewan da yayi mata be amfanar da komai ba sai na tafi zuwa mataki na uku.

  1. Mataki na uku:

Idan miji yayi kokarin gayra wannan mata nashi ta hanyar nasiha da wa'azi da kyawawan magana da kauta duka amma babu amfani sannan ya kaurace mata a wurin kwana amma duka shiru ya kuma bayyana mata rashin yardanshi da aikinta shima be samu nasaraba, to anan wurin an yardan ma miji daya ladabtar da matan da duka wanda banajin ciwo ba ko kuma yi mata wani lahani, hakika malamai inyi ittifaki akan wajabcin bin wannan matakai a jere wurin warware matsalar mace wanda ta bijire wanda sune wa'azi a matakin farko sai kaurace mata sannan idan bata gyara ba sai duka, Ada'u yace nace ma ibn Abbas menene duka mara cutar wa? Sai yace mun shine duka da asiwaki da makamantan su!! Hasanul basari yace: ma'ana duka bame tasiri ba. Dan Allah dai ya kai makaranci me daraja shin duka da asuwaki yakai ace masa duka na mugunta da rashin tausayi abunda bai wuce tsayin pensir ban a rubutu?

Idan dai kana daukan duka da pensir a matsayin duka na mugunta da rashin tausayi to kazoo mugani baki dayan mu dakai sau nawa muke gani a cikin gidajen talabijin na holanda da sauransu suna sawwara mana labarin miji wanda yayi fishi da matar sa ko kuma tsakanin sa da abokin sa ko kuma wata mata ko shugaban kamfani da ma'aikacin sa wanda muke gani a cikin labarin wannan mutumi zai daura yatsantsa manuni akan kirjin sa yana masa kashedi ko kuma sanya pensir a kirjin sa wani loakci ma har abun yakai ga mari, hakan na faruwa cikin dayawa daga cikin finafinai idan miji yayi fushi da matar sa hakan na kaiwa ga mari me karfi a fuskanta sa'annan ya bar wurin, amma wannan dukkunin sa turawa basa daukan sa a matsayin mugunta kawai yanayi ne yakai mijin nan da marin matar sa, kuma kaga suna daukan wannan mutumi a matsayin mutum wayayye, duk da cewa mari a fuska haramun ne a musulunci sai dai suna fada ne da musulunci suna fadin karya akansa cewa yana koyar da rashin tausayi.

 Duk da cewa musulunci yaba namiji damar amfanin da ikon sa na ganin ya gyara wannan mata cikin matakin farko dana biyu sannan na uku lallai musulunce yaba wannan matar hakki na neman saki tun kafin akwai ga wannan mataki abunda yake kira da suna khul'i idan ta iatce ta nemi hakan daganan kuma sai ta yanke ma kanta hukunci inane zata gaba: wannan shine abunda zamuyi magana akansa nan gaba da yardan Allah madaukaki.

Masani fa cewa nasiha da kauracewa sannan duka bashi bane hanyar warware matsaloli nay au da kullum ba tsakanin ma'aurata, wannan hanya ce ta warware manyan matsaloli a tsakanin su, misali da ace miji zai cema matar sa ki girka mana shinkafa yau da kifi sai ta manta ta girka shinkafa da kaza shin wannan ayar zai tabbata akanta da yayi mata nasiha sannan ya kaurace mata sai kuma duka?!!!!

Amsar itace a'a, wannan al'amura ne kanana wanda ya wajaba a rika yafiya akai ba tare da ladabtarwa ba, amma kuma idan matan ta kasance bata da halaye na gari me girman kai sannan mijin ya fara ganin ta fara ayyuka na bijirewa da girman kai da saba masa!! Mu anan muna magana ne akan mace wanda ta bijire wacce take bukatan nasiha da shiryarwa da magani akan matsalolinta kamar mara lafiya ne wanda yake bukatan magani, muyi kaddar cewa wannan mata wanda ta bijire mijin yayi nasihar da kauracen wa da duka na tsawon lokaci taki gayruwa shin sakinta shine yafi ko kuma duka wanda bana cutarwa ba?!!!! Idan duka ya kasance harara gefe shi kuma saki makanta to lallai me harar gefe yafi makaho kuma da za'a bar wannan mata akan halinta zata tarwatsa iyalan nan da al'umma baki daki!!

 

 

Babi na biyar

Ma'ana da kuma abunda duka yake nufi a cikin musulunci.

Tun gabanin kungiyar kare hakkin dan adam ta duniya ta gara yaki da mugunta tsakanin ma'aurata da yara hakika musulunci ya rigata da hakan yadda yayi yaki dashi ya kuma haramta shi da tanadar wa me aikata hakan da ukuba nan duniya dana lahira bawai haramta hakan ya tsaya bane akan aikin kawai a'a hatta magana wanda ya shafi hakan yana cikin wannan haramci wanda hakan yafi zama kamala akan dokokiwanda suke yin ukuba na duniya kawai tun gabanin shekaru 1400 da suka wuce manzon Allah s.a.w yace:" Ahmad da tirmizi ne suka rawaito hadisin, albani kuma ya ingantashi.

Ya kuma kara cewa har wayau:. Buhari ne ya rawaito shi cikin adabul kadi da tirmizi kuma albani ya inganta shi.

Me tambaya zai iya tambaya cewa ta yaya musunci ya hana mugunta amma kuma ya halatta miji ya duki matar sa?!!

Game da amsan wannan tambaya ya kamata muyi bayani a farko banbanci tsakanin abunda duka yake nufi a cikin rayuwan mu ta yau da ma'anarta a cikin shari'ar musulunci, a cikin rayuwan mu tayau idan mutum yaji cewa mutum ya duki matar sa abunda zai zo a tunanin sa shine wannan aiki na rashin tausayi ne da mugunta da zalumci na wannan miji wanda yakai sa da dukan matar sa sannan yanayin wannan mata da mijinta ya zalumta da duka shine ya jijji mata ciwuka dukkanin jikinta da karaya, wannan shine ma'anar duka a rayuwan mu ta yau wanda muka samo shi dilimin mu da rayuwan mu da cewa shine misalign daya duki matar sa, amma idan nace maka na duki karar rawan kowa shin zata fahimci cewa tana ta'addanci ga wannan kofa?!! Sannan idan nace maka zan duke misali shin zaka fahimci cewa zan maka ta'adi ne irin haka?!! Kenan Kalmar duka tana cancanzawa gwargwadon yadda akayi amfani da ita a harshen wannan mutane da kuma dabi'ar wannan mutumi dukkanin wannan zai zo cikin tunanin mu akan ma'anar duka, saboda haka ma'anar duka a musulunci yasha banban gabaki daya da ma'anar sa cikin rayuwan mu nay au wanda hakan haramun ne kuma ta'addanci ne a cikin musulunci sosai, wannan ma'anonin bazasu taba haduwa ba har Abadan idan munason yin adalci saboda haka ya wajaba muce babu dukan mata ga miji acikin musulunci kuma ba'a yardan masa da wulakantata ba ko kuma muzguna mata ko yi mata magana da kalamai marasa dadi, ma'anar duka a musulunci yana nufin duka dan kadan kamar misalign dukan karar rawa wanda ake nufin isharantar da matan dashi da cewa lallai tanayin kuskure cikin hakkin mijinta sannan kuma mijin yanada hakki na gyarata da daidaita ta, kuma hakika musulunci ya gindayawa miji matakai na warware matsalolin mace wanda ta bijire wanda matakai ne da suke gabanin duka ya sanya duka shine shine mataki na karshi ga duk macen da bata gyaru ba har zuwa wannan mataki, kuma musulunci ya zo da tsawatar wa da hukunce hukunce na shari'a ga mijin da ya wuce gona da iri yadda zai zama me sabo me ketare iyakokin Allah madaukaki wanda ya cancanci a azabtar dashi duniya da lahira wannan matakai kuwa sune:

 

 

Dokokin ladabtar wa da duka:

  1. Bi mataki bayan mataki wurin warware matsala ta hanyar yin kokarin sa wurin matakai na farko dana biyu wanda suke gabanin duka da yin wa'azi da fadakarwa sa'annan kaurace mata a wurin kwana.
  2. Dukan ya kasance da asiwaki ko kuma makamancin haka wanda dan kara ne da be wuce tsayin pensir din rubutu ba da fadin sa.
  3.  Nisantar fuska wurin duka ko kuma gabban da ake ji dasu, saboda musulunci ya hana dukan fuskar na miji ne ko mace ko kuma dabbobi, saboda fuska tana da daraja sannan kuma taba shi yana cutar da ganin mutum kamar yadda aka haramta dukan gabbai wanda ake ji dasu na jiki kuma an tsananta akan hakan, wannan sune iyakokin Allah duk kuma wanda ya ketare su to yayi zunubi.
  4.  Wurin dukan kada ya zama a idon mutane cikin ko wani hali, baya halatta miji ya duki matar sa a gababan mutane musamman yaransa, saboda hakan akwai wulakanta matar acikin sa a karon farko sannan kuma jawo lallacewar tarbiyyan yaran, wani irin tarbiyya ce wannan uba keyi da dukan mahaifiyar su a gaban su ko kuma a kunnan su?!!!
  5.  Kada dukan ya zama me cutarwa wanda zayyi mata tabo a jiki ko kuma karaya ko ciwo, duk mijin daya jima matar sa ciwo ko tabo ko karaya yayi zunubi kuma wannan miji mugu ne me bushashen zuciya wanda bayason gyaruwan matar kawai hukuntata yake sonyi sannan kuma ya jawo kiyayya sannan kuma shari'ar musulunci me adalci ta wajaba a tuhume shi da kuma hukunta shi akan haka.

 

 

Babi na shida

Dukan mace cikin sauran addinai

 Lallai maganar dukan mace ba matsala ce wacce ta shafi wani lokaci ba ko zama daya kawai ba cikin al'umma guda daya, a'a wannan matsalatra kwaita cikin dukkanin al'ummomi na dukkanin zamani baka daya, kuma duk wanda yakeson sani darajar mace cikin al'ummonin da ana samun littattafai dayawa wanda sukayi magana akan hakan, game da darajar mace kuma cikin al'ummar girka da rumawa da china da hindiya na da can… zuwa dai karshen su, sannan kuma akan haka yaya addinin yahudanci da kiristanci suka mu'amalaci al'amarin dukan mace wacce ta zama matsala wanda aka saba kuma tana yaduwa cikin al'umma tsofaffi har zuwa al'ummar shugaban mu almasihi, shin shugaban mu almasihi amincin Allah ya tabbata a gareshi yayi magana akan haramcin dukan mace koda sau daya?!!! Kuma shin akwai nassoshi cikin littattafai masu tsarki ltsohon alkawari ne ko kuma sabon alkawari wanda ya haramta ko kuma kyamatan dukan mace?!! Bayan bincika zai bayyanan maka cewa babu wani abu wanda yake nuna haka.

Idan kirista ya duki matarsa shin yayi sabo sannan za'a hukunta ta fuskan addini wanda hakan itace ukubansa wanda nassi yazo dashi cikin littafi me tsarki? Hakika bayi sabo ba saboda babu wani nassi wanda yake nuna hakan cikin littafi masu tsarki shin tsohon alkawari ne ko kuma sabon alkawari!!

Kamar kuma yadda babu wani hukunci ta bangaren doka na ukuba akan mijin daya duki matar sa sai dai idan alamar ta'addanci ya bayyana a jikin matar kamar karaya ko kuma kunburi ko ciwo, amma idan babu wani alama wanda ya bayyana a jikinta to tayaya za'a tabbatar da dukan nan nashi dayayi mata!!! Ma'ana idan yayi mata duka wanda babu ciwo ko karaya acikin sa baza'a mai wani ukuba baa nan duniya ko kuma cikin dokakin su!!!

Mu duba mugani cikin yahudanci da buzanci shin akwai wani nassi wanda yake haramta dukan mace?!!!

Hakika babu wani nassi na addini cikin ko wani addini wanda yake haramta dukan mace sai cikin musulunci kadai!!!!!! Kafin ko bayan dukan mace ya tashi daga hukuncin haramci ne zuwa makaruhanci dukda haka dai musulunci shi kadai ne wani addini wanda ya nassanta akan kyamar dukan mace!! Amma sauran addinan babu furta ba kai tsaye haramci ko kuma kyaman haka a wurin su.

Kamar yadda babu wani addini wanda ya shinfida dokoki ya iayaka wurin dukan mace sai musulunci kawai, watan ma'ana idan miji kirista ya kasa mallakan zuciyar say a duki matan sa, to menene tsari ko kuma iyaka wanda baya halatta ya ketare su? Shin kiristanci ya nassa akan dokoki da iyaka ga miji na dukan matan sa kamar ace kada ya duki fuskanta ko kuma yayi mata rauni wanda zai bar mata tabo ajiki… da sauarn su? Hakika babu hakan.

Duk me lura da rayuwan mu nay au wanda muke ciki sai ga akwai wasu adadi na kiyasi game da dukan mata wanda mazan kiristoci sukeyi ko kuma yahudawa ko kuma sauran su wand aba musulmai ba, kaje ka bincika cikin hukunce hukunce da kararraki a gaban yan sanda ko kuma kotu a amerika da kasashen turawa zakaga adadi wanda aka kiyasta na dukan mata wanda mazaje marasa tausayi suke yima matan su da yaran su!!!

Hatta a cikin al'ummar jihiliyya gabanin zuwan musulunci zaka samu cewa larabawa suna zane matan su irin bulalan da sukeyi ma bayin su kuma hakan ya zama sananne ko al'ada wanda ba haramun bane ko kuma akwai hukunci akan haka na wani shari'a ko kuma wani doka, a lokacin da aka aiko Muhammad s.a.w ya hana wannan aiki hanawa me tsanani sai yacebuhari da muslim ne suka rawaito shi amma lafazin na buhari ne, a cikin wannanhadisi manzon Allah yana raddi game dukan matar sa cd rana sannan kuma da daddare yana neman ya kwanta da ita!! Watan ma'ana taya zaka zama mugu me baki hali da ita da rana amma kana son ta manta hakan da daddare ka lallashe ta!!.

 

Abubuwan da aka kalato game da darajan mace cikin littattafai masu tsarki cikin tsohon alkawari da sabon alkawari:

Sau dayawa abunda mutanen addinin kiristanci suna sawwara mana shine shugabammu almasihi amincin Allah ya tabbata agareshi shine mutumi na farko wanda ya fara karewa mace hakkokinta kuma shine wanda ya bata hakkokinta wanda babu wani addinin da suka bata irin sa, kuma littafi me tsarki ya mata adalci sannan ya kuma daga darajarta!!! Sai dai kuma shin wannan maganar yana daidai da aikin mu na yanzu?!!!

Kowa ya sani cewa littafi me tsarki ya haramtawa mace shiga cikin tsarin shugaban cin coci wanda shine shugaban masu tsarki ko kuma meyin yankan me tsarki, shin wannan mace karama ce ko budurwa ko tsohuwa, al'amarin bashi da alaka da shekaru ko kuma jinsin mata, babu wani littafi cikin littattafai amsu tsarki na tsohon alkawari ko kuma sabon alkawari wanda yayi ishara da shigan mace cikin tsarin shugabancin coci, bare kuma a bata daman a zama cikin malaman addini, mace asali ma ba'a mata izinin magana ba a cikin coci ko kuma karantan wani abu cikin coci kuma ba'a bata izinin neman wani matsayi ban a manyan malaman coci kawai matsayin da aka yardan mata da nema shine mataimakan malamai wanda matsayi ne nayin hidima ga malamai!!!!! Hakika littafi me tsarki ya gabatar mana da nau'oka na malaman su dukkanin su mazaje ne shin manyan malaman ne na farko kamar Nuhu da Ayyub da Ibrahim da Ishaq da yakub, ko kuma kuma malaman haruniyya ne ko kuma malaman malikus sadik, ko kuma malaman manzanni da khalifofin su na kasa kasa, dukkanin su mazaje ne, sannan da ace za'a ba mace matsayin malanta da shugabarmu Maryam akaba itace tafi cancanta da wannan matsayi sai dai karkashin karantarwan addinin kiristanci an haramta ma mace haka!!!!!

 

Bari mu kawo wasu daga cikin nassoshi cikin littattafai masu tsarki domin muga matsayin mace a cikinta da darajar ta:

 

  1. Mace ana azabtar da ita da laifin namji:

Safar na Irmiya (23:34): " annabi ko kuma wani mahaluki ko mutanen da yake cewa: wahayin Allah, za'a azabtar dashi da iyalin sa"

  1.  Kona mace mazinaciya da wuta:

Safar al lawiyyin (9:21): " idan wani mahaluki ya tayi sabo na zina to hakika tayi datti a kona ta da wuta"

  1.  Yanke hannun mace da wasu dalila wanda hankali baya dauka:

Safar al tasniya (11:25): " idan mutane biyu sukayi fada da juna mutum da dan uwan sa sai matar daya daga cikin su tazo wurin domin ta kwaci mijinta sai hannunta yayi tazar ce ta kama al'aurar sa, za'a yanke mata hannu kuma za'a tsire idanun ta".

  1.  Macen da aka saketa da ita da tsohuwa mara aure da mazinaciya duka daya ne:

Safar al lawiyyin (9:21): " duk wani mutum me girma ….., wannan yana auren mace ce tsarki. Ita kuma mace tsohuwa mara aure ko wanda aka saka ko me daddi ko mazinaciya to kada ya aure daya daga cikin su, sai dai ya aure masu tsarki daga mutanen sa, sannan kuma kada ya bata shukar sa a tsakanin kafafuwar sa saboda ni ne ubangiji me tsarki".

  1.  Bautar macen da aka saka ga mijinta:

Sakon bulus zuwa ga mutanen afsis (5:22): "yaku mata kuyi bauta ga mazajenku kamar ubangiji, saboda namiji shine shugaban mace kamar yadda masihi shine shugaban coci kuma shine me tsarkakejiki. Sai dai kamar yadda coci take bauta ga masihi, haka mata zasu rika bautan mazan su cikin komai"

  1. Wajabtawa mace yin shiru cikin coci:

Sakon bulus na farko zuwa ga mutanen kurunsus (14:34): " matan ku su rika yin shiru a cikin coci, saboda ba'ayi mata izini ba da magana kawai bauta zasuyi kamar yadda namus yace. Sai dai idan suna son sanin wanin abu to su tambayi mazajen su a gida, saboda abun kyama ne ga mace tayi magana cikin coci".

  1. Mata sanadi ce ta bata:

Sakon bulus na farko zuwa ga timosayis (11:2): " mata su koyi shiru cikin bauta. Sai dai ba'ayima mace izini ba da neman ilima ko kuma ta shugabanci namiji, ta zauna shiru kawai, saboda adam aka fara halitta sannan sai hauwa. Kuma adam beyi laifi ba mace ce tayi laifi sai ta'addanci ya auku. Sai dai wannan zunubi nata zata tsakaka daga garesu da haihuwan yara matukar sun tabbata cikin imani da so da girmamawa tare da hankalta"

  1. Shugabantan namiji ga mace:

Sakon badris na farko (3:1): " gare ku yaku mata ku zama masu bauta ga mazajen ku… taka adon ku ya zama irin adon wace, na bude gari da sanya zinari da tufafi, sai dai mutumin zuciya na biye wurin tabbatar da farna, adon rai da bankwana na tsanake, wanda sune kafafuwan allah masu yawan nauyi.haka mata suka asance ada can masu tsarki da tawakkali ga allah suna gyara jikin su suna bauta ga mazajen su, kamar yadda saratu tayima Ibrahim biyayya tana me kiransa da "shugabana".

Safarul takwin (3:16): " sai mace tace: ina wahala dayawa wurin daukan maka ciki da Haifa maka yara kuma ga kafafunka nake biyayya"

  1.  Jifar mace mazinaciya har sai ta mutu:

Safar al tasniya (22:13): " idan mutum ya aure mace lokacin da yayi amfani da ita sai yaji ya kita, ya kuma jingina mata dalilan magana, sannan yayi ishara da cewa sunanta mayafi, sai yace: wannan matar na rike ta kuma nayi zunubi da ita ban sameta da budurci ba, sai uba da uwa su dauki yarinyar su su fitar mata da alamar budurci zuwa ga malaman garin zuwa ga kofa,… sai malaman wannan gari su dauki wannan mutum su ladabtar dashi suci tarar sa na azurfa dari,… sai dai idan wannan al'amari ya kasance ingantacce ba'a sami budurci ba ajikin yarin yan. Sai a fitar da ita zuwa kofar gidan babanta mazajen wannan gari su jefe ta da duwasu har sai ta mutu".

Safar al tasniya (22:22): " idan aka samu wani mutum kwance da wata mace matar wani, to a kashe su biyun: namijin daya kwanta da matar, sai a cire sharri daga isr'il".

Safar al tasniya (22:23): " idan mace budurwa ta wani ya nemi aurenta sai wani mutum ya sameta na daban ya kwanta a ita a cikin gari, to ku fita dasu zuwa kofar wannan gari ku jefe su da dutse har sai sun mutu".

  1. Mace tana kasa da namiji a daraja:

Sakon bulus na farko zuwa ga mutanen kurnunsus (11:3): " inason ku sani cewa shugaban ko wani namiji shine masihi, shugaban mace kuma shine namiji, shugaban masihi kuma shine Allah. Ko wani mutum da yake salla ko ya zama annabi to akan sa akwai abu wnada wulakanta kansa, amma duk mace da take salla ko annabta kanta abude to ta wulakanta kanta saboda da ita da wanda aka aske abu daya ne. idan mace ta zama bata rufe kanta to a rake mata gashin kanta, idan kuma ya kasance abun kyama ga mace a rage mata gashi ko kuma aski to ta rufe shi. Baya halatta namiji ya rufe kansa saboda kasancewar sa surar allah da kokarin sa. Ita kuma mace kokarin namiji ce, saboda namiji ba daga mace yake ba ita macen ce take daga namiji. Kuma saboda na miji ba'a halicce sa ba domin mace, ita macece aka halitta domin namiji. Saboda haka ya wajaba ga mace ya zama akwai shugabanci akanta saboda da mala'ika."

11. karantar da mata littafin diskoliyya (littafe ne wanda ya kunshi karantar da ubangiji da manzanni):

Babi na biyu cikin littafin diskoliyya me maudu'in (ya wajaba akan mata su bautawa mazajensu kuma su rika tafiya ka hikima) yana cewa: " mace tayi ma mijinta bauta domin shine shugabanta,… kiri tsoron mijin ki ke mace, kuma ki rikajin kunyar sa da neman yardan sa shi kadai bayan Allah, kamar misalign abunda mukace, ki hutashe dashi wurin maki hidima domin ya jawo zuwa gareki,…. Idan kina son ki kasance mumina wanda Allah ya yarda da ita kada ku rika kwalli domin samarin mazaje su yarda, kuma kada ki rika sha'awar riga mara nauyi masu nauyi wanda basu dace da kowa ba sai mazinata domin wanda suke son ki kasance a haka su rika binki. Idan kun kasance bakwa aikata wannan ayyukan masu muni saboda zunubai to ki rika kwalliya ke kadai domin addini saboda da haka ne zaki tsagu ga wanda zai ganki yayi sha'awarki, to me yasa bazaku kiyaye ba domin kada ku fada cikin zunubi, kuma kada kusa wani yafada cikin shakka ko kuma kishi domin ki, idan kinyi kuskure na daurewanki akan wannan aiki to lallai zaki fadi, domin kina gina sababi ne na halakar da ran wannan mutumi. Sannan idan kayi kuskure ga wani akan wannan aiki lokaci daya shi kuma zai kasance sababi na kayi kuskure ga mutane dayawa, ke kuma kina cikin karanci kwadayi, kamar yadda littafi me tsarki yake cewa: (idan munafika ya fada cikin sharrukan mutane dayawa to lallai yana sani da kuma yawowa masa radadi da kunya), duk wacce take aikata haka zata halaka da zunubi sannan kuma zata farauto zuciyar maza ba tare da kayan farauta ba, ku karanci abunda littafi me tsarki yake cewa game da wanda yake kirkira akan wannan mutane kamar haka cikin fadin sa: ( kanakin mace me zunubi sama da mutuwa, wannan dinnan da ta zama abun farautan jahilai), ya kuma kara fada a wani wuri na daban: ( misalign tsutsan da yake cin katako, haka mace me zunubi take halaka mijinta) ya kuma kara fada cewa: ( abunda yafi shine zama a lungun saman gida sama da zama tare da mace me datti mara kama kai). Kada kuyi koyi da irin wannan mata, yaku matan misihi idan kuna son ku kasance muminai to lallai ku himmatu da mijinki domin samun yardan sa shi kadai. Kada kawata fuskar ki da Allah ya halicceta, babu abunda yake rage kwalliya, soboda dukkan abunda Allah ya halicce sa yana da kyau sosai, baya bukatar kwalliya, duk abunda ya karo akan kyau to lallai yana canza ni'imar mahalicci. Idan kina tafiya ya kasance kina kallon kasa bayan kin rufe jikinki baki daya, ka nisanci dukkanin wani aboki wanda be cancanci kasance wa abayi ba tare da mazaje, da yawa abokan fasikanci ne, kada mace mumina ta rika cudanya da maza. Sannan kuma idan zata rufe fuskarta ta rufeshi da tsoron kallon maza samari… abunda ya wajaba agareki idan kin kasanc emumina shine ki guji dukkanin nau'i na kari, da kuma kallon idanu dayawa… (lallai zama a daji yafi alheri da zama da mace me dogon harshe mara tarbiyya)".

 

 

Babi na bakwai

Dukan mace cikin al'ummar yamma na kiristoci

Makiya musulunci dayawa sunyi kokarin yada wasu shubuhohi game da musulunci daga cikin su akwai maganar dukan mace suna amfani da almakashin su na sirihi wanda suka saba yadda suke hakaito wa daga cikin ayoyin alkur'ani me girma da hadisan manzon Allah s.a.w dukkanin maganar da shubaha zai ina hawa kansa tare da tabbatar da abunda zai tabbatar da wannan shubuhar nasu, kamar duka a cikin musulunci misali sais u ambaci tsurar maganar kawai ba tare da Ambato maganar da yake gaban sa ba ko bayan sa suna kokarin kawo shibuhohi na karya akan musulunci da dabarar su mummuna wacce tayi nisa gabaki daya da gaskiya da maudu'i, baza su kawo maudu'in ba baki dayan sa sais u yanke sa wanda za'a masa mummunan fahimfa, musa yin wannan aiki suna kirkiran karya ga musulunci da ikirarin wayewar su da warkewan su wurin mu'amala da mace da matan sun a gida, sai dai a hakika sun rufe idon su akan wasu gaskiya da hakika masu zuwa:

Na farko: lallai musulunci shine addini daya tilo wanda yayi bayani akan alaka ta rahama da soyayya tsakanin ma'aurata, kuma shine addina daya tilo wanda yah aka ta'addanci da cuta na magana ne ko kuma aiki, Allah madaukaki yana cewa: " kuma daga cikin ayoyin say a halitta maku mata daga kawunan ku domin ku samu natsuwa zuwa gare su ya kuma sanya soyayya da rahama atsakanin ku"

(suratul rum ayata 21)

Amma fa musani cewa wannan soyayyar da rahama bata zuwa sai bayan daurin aure ingantacce wanda ya halatta a shari'a.

 

Na biyu: lallai musulunci shine addini daya tilo wanda ya magance duka da wulakantar da mace da kuma kallonta da idon nakasa tun shekaru dubu daya da dari hudu da suka wuce a baya ya kuma irga hakan daga cikin ayyukan nakasu ga maza.

Da ace zamu bincike na keke da keke cikin littattafai masu tsarki na kiristoci tsohon alkawari ne ko kuma sabon alkawari bazamu samu ishara ba akan haka na kusa ko kuma ta nesa wanda yake haramta dukan mace.

 

Na uku: lallai musulunci ya kwadaitar da yin mu'ama na karamci ga mata cikin dukkanin ayoyin alkur'ani da hadisai masu daraja wanda suke magana akan alaka tsakanin ma'aurata, Allah madaukaki yace: " suma sunada irin abunda kuke dashi akansu a wurin na kyautatawa"

(Suratul bakara ayata 228)

 

Na hudu: lallai musulunci ya sanya mu'ama ta mutane ta jin kai musamman tsakanin ma'aurata daga cikin ayyukan da suke jawo lada da sakamako, manzon Allah s.a.w yace: buhari da muslim ne suka rawaito shi.

 

Na biyar: lallai musulunci ya halalta dukar mace a wasu lokuta bawai ka'ida bace sannan kuma gindaya wasu sharudda ga miji wanda zai farayin su kafin duka wanda shine mafita na karshe sannan kuma dukan ya kasance kare barna ne babba, saboda kasancewar mata ba'a yanayi daya suke cikin dukkanin zamani da al'umomin da iyalai. Abunda zai iya daidai da wannan al'umma ba dole bane yayi daidai ga wasun su kila ma su ya cutar dasu ne, sannan abunda zayyi daidai na mu'amala da wani mace bazai zama yayi daidai ga waccen macen ba cikin wani al'umma ta daban ko kuma cikin zamani na daban duk yadda kayi kokarin sanya shi ya dace da ita kuwa, hakan yana cikin gamayyar muslumci da karade dukkanin al'amura.

 

Na shida: lallai zahirin mugunta na zamanta kewar iyali ya yandu cikin garuwan mutane da kasashe wanda sukaci gaba da wanda basuci gaba ba cikin wannan zamani namu, maza nawa ne na kiristoci turawa suke yin ta'addanci a fili ga matan su a gaban mutane a filin jirgi ko wurin cin abici ko wani wurin taruwa na daban kai hatta akan tituna manya a gaban wurin wucewar mutane ana samu hakan bawai a asirce akeyin su ba a'a takai ga har a gidajen yada labarai wanda ake gani da wanda akeji duk suna kawo wannan labari.

Kuma mata nawa ne na kiristoci cikin turawa cikin Amerika da kanada da austreliya wanda suka ware bangare nay an sanda domin fuskantar aikin ta'addanci akan mata na duka gada mazajen su, sannan wannan shari'ar bazata yiwu ba sai ansamu alamomi na fili kamar yadda mukayi bayani a abaya kamar karaya ko kuma kunburan kasan ido ko tabo a fuska saboda da wannan duka, duk wanda ya bincika cikin hasashe na gwamnati na bangaren yan sanda cikin amerika da kasashen turawa da austireliya hakan zai bayyanan masa.

 

Yaduwar alamar duki cikin a'umma yamma:

Abunda yake bayyana yaduwan mugunta na iyalai cikin kasashen yamma wanda suke ikiraren wayewa da ci gaba na hakkin dan adam bana arziki ba abubuwa ne Kaman haka:

  1. Yaduwar kungiyoyi na hukuma da wanda bana hukuma ba cikin kasashen turawa wanda suke kurmushe matsalar ta'addanci ga mata da muguntan iyalai wanda sashin shari'a ta kasa magance masu hakan na zalumcin mazaje akan matan su.
  2. Wannan sanarwan da ake nanatawa akoda yaushe cikin kafafen yada labarai wanda ake gani da naji wanda suke kwadaitar da isar da hukuma cikin gaggawa game da duk wani labari na ta'addancin daya daga cikin ma'aura ta ga abokin zaman sa.
  3. Tambayoyin da akeyima daidaikon al'umma a koda yaushe na kasashen yamma wanda daga cikin su akwai:

Shin ka taba dukan matar ka ko sau daya ne?

Shin ka taba gani ko ji a wata rana ko sau daya ne babanka ya duki mamarka?

Shin ka tabaji abaya cewa wani daga cikin yan uwanka ya duki matar sa?

Shin ka tabajin daya daga cikin makwabtar ka ya duki matar sa?

 

Abun nufi na yin wannan tambayoyi ga mutane shine anason tabbatar da afkuwar samun ta'addanci ga mata daga mazajen su kiristoci cikin dukkanin kasashen turawa da amerika da Canada da austireliya, kuma wannan shine zahirin abunda yake yaduwa a tsakanin su dayawa.

A karshe falalar musumci ga mace zai bayyana ga dukkanin mutum me adalci kasancewa shi kadai ne addini daya tilo wanda ya karrama mace ya kuma daga darajarta da sunanta daga dukkanin wanda yake toye mata karamarta yake kuma jarabtar kamewarta sannan kuma yayi tsoratarwa babba game da zalumtar mace, manzon Allah s.a.w yace: Ahmad ne ya rawaito shi da nasa'i da ibn majjah kuma yana cikin littafin sahihul jami'u 2447.

 

 

 

Karshen littafi:

Lallai musulunci shine sakon Allah dawwa mamme wanda ya aiko da ita zuwa ga mutane baki daya akan harshe Muhammad s.a.w, kuma hakika wannan sakon na ubangiji ya bayyana falalar mutum akan sauran halittu wanda Allah ya halitta tun farkon saukan sa, Allah madaukaki yace: " hakika mun karrama dan adam kuma mun sanya shi a bayan kasa da cikin rafi sannan kuma muka azurta shi daga dadaden abubuwa sannan muka daukakashi akan dayawa daga cikin halittun mu (70)"[161].

Bayan Allah madaukaki ya bayyana ma mutum kimar sa cewa fay a daukakashi akan halittun sa dayawa sai ya bayyana wani ka'ida na daban wanda itace daidaito tsakanin dukkanin mutane a mafarin halitta, Allah madaukaki yace: " yaku mutane kuji tsorn ubangijin ku wanda ya halicce ku daga mutum daya"[162].

Daga wannan asali ne mutum zai kasance daidai yake da dan uwansa cikin kima ta dan adam kowa an bashi yancin fadin albarkacin bakin sa da ra'ayin sa da kuma amfani da abunda Allah ya sanya cikin wannan duniya na ni'imomi da alherai ko da kuma akwai banbanci a tsakanin sun a asali cikin dangankatar su da launi fata, koda kuwa yanayin rayuwan su yasha banban hakan baya nufin sun banbanta bane a asalinsu nay an adam falalar su a wurin Allah da wanda yafi wani acikin su a wurin bawai ya ginu bane akan banbancin launin fatar su ko yare, dukkanin su a wurin Allah daya suke mazan su da matan su me kudi da talaka me mulki da mara mulki kawai suna samun banbanci ne a tsakanin su gwargwadon nisan su da kusancin su na aiwatar da shari'ar Allah da kuma tsayawa akan hanya ta kwarai, Allah madaukaki yace yana me magana ga mutane da bayyana masu wannan asali nasu: " yaku mutane lallai mun halicce ku daga maniji da mace sannan muka sanya ku kabilu da mutane dayawa domin ku samu sanayya a tsakanin ku, lallai wanda yafi wani a cikinku daraja awurin Allah shine wanda yafi ku tsoron Allah"[163].

Karantarwan musulunci ta ajiye mutum da dan uwansa a daraja daya cikin asalin halitta da kima ta dan adam, ta kuma daidaita mace da namiji cikin dukkanin al'amura sai wanda bukata bayyananne ya kawo a kebance, Allah madaukaki yana cewa: " muminai maza da muminai mata sashin su masoya sashi ne"[164].

Ya kuma kara fadi cewa: " sai ubangijin su ya amsa masu addu'ar su da cewa lallai ni bana tuzarta aiki wani daga cikin ku namiji ne ko mace"[165].

Kuma ina ga yadace ya kawo wasu daga cikin hatsarori a takaice:

  • Zan iya cewa ina kuma da tabbaci da hujjar maganata cewa mace bazata taba jin dadin hakkokinta ba da yancin ta na dabi'a cikakke sai a karkashin inuwar musulunci saboda kasancewar sa addini ne daga sama wanda mahaliccen mutum mazan su da matan su masanin halyen sun a duniya da lahira ya kawo shi.
  • Baya halatta mu rika yin hukunci akan musulunci sakamakon ayyukan wasu mutane musulma, dayawa daga cikin su suna jingina ne da musulunci amma sub a komai bane cikin musulunci saboda musulunci ba kawai furta Kalmar shahada bace kawai a'a musulunci akida ce da kuma aiki, misali zamu samu wasu daga musulumai wanda suke karya da ha'inci da kuma aikata wasu ayyuka masu muni hakan bawai yana nufin musulunci bane ua umurce su da hakan ko kuma ya yarda da abunda suka aikata!!! Musulunci gidane babba wanda daga cikin musulmai akwai wanda yake aiki da dukkanin karantarwan sa har sai ya kusan kaiwa daraja ta kamala amma kuma daga cikin su akwai wanda yake sakaci na aikawa wasu daga cikin ayyukan daya saba masa wanda ya cancanci ukuba da hakan nan duniya da lahira sai dai kuma hakan baya fitar dashi daga cikin rigan musulunci shine abunda ake kira da suna musulmi me sabo da zunubi.
  •  Kira ce wanda nakeyin ta ga duk wand aba musulmi ba da ya kasance yana da hukunci na kashin kansa bawai ya rika bin tunanin wasu ba ba fadakarwan su, kuma ya rika karanta littafi wanda aka yarda dasu me inganci akan musulunci domin sanin musulunci da tsarin sa a cikin su da cewa fa addinin Allah ne duk wanda ya karanta shi ba tare da son zuciya ba da kabilanci makauniya yana me neman sanin gaskiya to lallai ina tabbatar masa da cewa da yardan Allah zai haskaka masa ganin sa kuma zai shiryar dashi hanya madaidaiciya ga wanda Allah yake son sa da alheri.

Wata marubuciya me suna L.Veccia Vaglieri tana cewa cikin littafinta me suna kariya ga musulunci, dukda cewa ita musulma bace [166]: domin nesantar munanan dabi'u da kuma kariya game da sakamakon sa ya zama dole ga mace musulma ta sayansa hijabi kuma ta suturta jikinta baki dayan sa inba wasu daga cikin gabbai ba wanda zai bayyana yancinta wanda yake laluri kamar ido da kafa, yin hakan bawai karancin mutunta mace bane ko kuma koye masu yanci na abunda suke so, a'a hakan kariya ne gare su daga sha'awar maza kuma wannan itace ka'ida tsohuwa wacce ta hukunta nesantar mata daga maza da kuma rayuwa na dabi'a wanda yake samuwa daga hakan wanda suka sanya kasuwancin karuwai ba'a sansa ba baki dayan sa a kasashen gabas sai dai inda baki suke da mulki da iko a ciki, idan ya zama cewa babu wanda zai iya inkarin kimar wannan dabi'u to ya zama wajibi akan mu ya ciro cewa al'adar hijabi ta kasance asali me fa'ida wanda bashi da kudi na musamman cikin al'ummar musulunci.

Karshen kiran mu shine godiya ta tabbata ga Allah ubangijin talikai.

 

 

../../../../../../../Documents/MY%20SITES%20&%20PROJECTS/PROJECTS%20&%20SITES/ISLAML

www.islamland.com

 

 

 

Suratul hujurat ayata 13 [1]

[2] Idan bah aka ba me yasa basa kira da abi hakkokin wanda ake kashewa a kuma kona gidajen su da korar su daga ciki a kuma kwace masu dukiya? Kuma me yasa baza kira da hakkokin masu fama da yunwa da rashin lafiya cikin wasu kasashe talakawa? Muna kira da nema a wurin su da su daina shiga tsakiya suna haka al'ummar musulmai aikata abun da Allah ya umurce su na gabatar da taimako da agazawa wanda basa neman komai daga hakan face lada agun Allah

Mujallar rayuwan muslumci nan gaba adadi na 146-[3]

Sahihul buhari, mujalladi na 2, shafi na 882[4]

Suratul zariyat ayata 49 [5]

Littafin qada wal qadri na sheikh Muhammad Mutawalli al-sha'arawy, shafi na 130-132 [6]

Dakta G.Lebon shafi na 488 [7]

Suratun nahli ayata 59 [8]

Suratul isra'I ayata 31 [9]

Suratul an'am ayata 139 [10]

Asfarul muqaddasa fil adyanul sabiqa na dakta Aliyu abdulwahid, shafi na 168 [11]

Maza hasirar alam bin khidadil muslimin na Nadawy yana me hakaito kissar muha baharati [12]

Kissar waewa na W. Durant, mujalladi na 3, shafi na 181,180,178, tarjamar Muhammad badran [13]

Wayewar larabawa na Dr. G. Lebon, tasirin musulunci cikin halayen mata a gabashin duniya, shagfi na 406 [14]

Asarar me akayi da kate musulunci na Nadwy ya nakalto daga R.C. DUTT 331 [15]

 Mace a cikin china na W. Durant, mujalladi na 3 [16]

Mace a cikin china, mujalladi na 4 [17]

Wayewan larabawa, shafi na 406, tarjamar za'ir [18][18]

W. Durant, mujalladi na 1, shafi na 119 [19]

Kisar wayewa, mujallladi na 9, shafi na 118,119,120 tarjamar badran [20]

Mukaranan addinai na dr Ahmad shulbi, shafi na 188, da kuma littafin wayewan larabawa shafi na 408, tarjramar za'ir [21]

 Wayewar larabawa shafi na 406 [22]

Wayewar larabawa tarjamar za'ir, shafi na 408[23]

Mukarana tsakanin addinai na dr Ahmad shalbi shafi na 186 [24]

Kissar wayewa mujalladi na 7, shafi na 117,118 trajamar Muhammad badran [25]

Shafi na 406 ta'arib na adil za'ir [26]

Dirasat fin tarik hadaratul yunan wal roman shafi na 149, na dr hussain al sheikh [27]

Safar takwin mujalladi 1/3 [28]

Al ishah assabi'u sakin layi na 25/26 [29]

W.Durant mujalladi na 2, shafi na 374 [30]

Safar al tasniyatul ishah 25 daga cikin safar al tasniya sakin layi na 5 [31]

Gamin dokoki da al'adar yahudawa da al'adu na al ha kham rabiy sulaiman jaza firayid shafi na 22 [32]

Muqaranatul adyan na Ahmad alshulbiy shafi na 187 [33]

Sabon alkawari daga cikin sakon bulus manzon farko zuwa ga mutanen kurunthus sakin layi na 3-7-9, shafi na 280 [34]

Sabon alkawari daga cikin sakon bulus zuwa ga mutanen afsis sakin layi na 22, shafi na 317 [35]

Suratun nahli ayata 97 [36]

Suratun nisa'I ayata 1 [37]

Sunan abi dawud mujalladi na 1, shafi na 61, lambar hadisi na 236, albani ya inganta shi [38]

Suratun nur ayata 4 [39]

Suratun nisa'I ayata 7 [40]

Suratun nisa'I ayata 19[41]

Sahihu muslim mujalladi na 2, shafi na 1180 lamba na 1479 [42]

Suratul bakara ayata 267 [43]

Suratul ahazab ayata 35 [44]

Sahihu ibn hibban mujalladi na 9, shafi na 483 lamba na 4176, albani ya ingantashi cikin sunan abi dawud [45]

Sunan ibn majjah mujaladi na 1, shafi na 81, lamba na 224, albani ya ingantashi cikin sahihu ibn majjah [46]

Muhari ya rawaito shi da ibn majjah da Ahmad [47]

Suratul taubah ayata 71 [48]

Suratul taubah ayata 6 [49]

Sahihul buhari mujalladi na 1, shafi na 14, lamba na 3008 [50]

Sahihul buhari mujalladi na 1, shafi na 141 lamba ta 350 [51]

Sunan al tirmizi mujalladi na 4, shafi na 141, lamba na 1579 [52]

Suratul an'am ataya 151 [53]

Suratul dalak ayata 6 [54]

Suratul bakara ayata 233 [55]

Sahihu ibn hibban lambar hadisi na 4240 [56]

Sahihul buhari lambar hadisi na 853 [57]

 

Sunan abi dawud lamabar hadisi na 2276 [58]

Sahihul buhari lambar hadisi na 5651 [59]

Sunan ibn majjah lamabr hadisi na 224 [60]

Sahihul buhari lambar hadisi na 4795 [61]

Suratun nahli ayata 90 [62]

Buhari da muslim ne suka rawaito shi [63]

Sahihul buhari lambar hadisi na 4843 [64]

Sahihul buhari lambar hadisi na 6546 [65]

Sahihu ibn hibban lambar hadisi na 446 [66]

Sahihu muslim lambar hadisi na 2630 [67]

Sahihu muslim lambar hadisi na 1623 [68]

Bazzar ya frawaito shi cikin kashaful astar hadisi lamba na 1893, da hasimi cikin mujamma'ul zawa'id [69]

Suratun nisa'I ayata 10 [70]

Mustadrak ala sahihain lamabar hadisi na 211 [71][71]

Suratul duha [72]

Sahihul buhari lambar hadisi na 4998 [73]

Dabarani ya rawaiyo shi lambar hadisi na 80 cikin sahihul jami'u [74]

Sahihul buhari lambar hadisi na 2334 [75]

Sahihu ibn hibban lambar hadisi na 4207 [76]

Sahihu muslim lamabar hadisi na 1218 [77]

Suratul dalaq ayata 7 [78]

Sahihul buhari lambar hadisi na 5049 [79]

Sunan akbaihaqi lambar hadisi na 15485 [80]

Sahihul buhari lambar hadisi na 1867 [81]

Musannaf abdulrazzak lambar hadisi na 12594 [82]

Sahihu muslim lamabar hadisis na 1437 [83]

Suratun nisa'I ayata 19 [84]

Suratul bakara ayaata 229 [85]

Sahihul buhari lambar hadisi na 3153 [86]

Sahihu muslim lambarnhadisi na 1469[87]

Sahihu ibn hibban lambar hadisi na 4176 [88]

Sahihu ibn hibban lambar hadisi na 4691 [89]

Sunanun nisa'I da dabari [90]

Surtaul bakara ayata 188[91]

Suratul shura ayata 38 [92]

Sahihul buhari lambar hadisi na 644 [93]

Sahihul buhari lambar hadisi na 4946 [94]

Sunan abi dawud hadisi lamba na 242 [95]

Sahihul buhari [96]

Mustadraka ala sihahain hadisi lamba na 244 [97]

Sahihu muslim lambar hadisis na 2761 [98]

Sunan ibn majjah hadisis lamba na 1996 [99]

Suratul isra'I [100]

Mustadrak ala sahihain lambar hadisi na 7248 [101]

Sahihul buhari lambar hadisi na 5626 [102]

Suratu lukman ayata 15 [103]

Sahihul buhari lambar hadisi na 5630 [104]

Suratu lukman ayata 15 [105]

Sahihu ibn hibban lambn hadisi na 429 [106]

Sahihu muslim [107]

Buhari ne ya rawaito shi cikin adabul mufrid [108]

Tirmizi da ibn majjah ne suka rawaito shi kuma albani ya inganta shi [109]

Sahihul buhari lambar hadisi na 3253 [110]

Sahihu muslim hadisi namba na 2549 [111]

Sahihul buhari lambar hadisi na 2477 [112]

Sahihul buhari lambar hadisi na 2152 [113]

Sahihu ibn hibban lambar hadisi na 435 [114]

Sahihul buhari, mujalladi na 2, shafi na 960, lambar hadisi na 2552 [115]

Sahihu muslim [116]

Sahihul buhari, mujalladi na 1, shafi na 182 lambar hadisi na 467[117]

Suratu Muhammad ayata 22 [118]

Sahihu muslim mujalladi na 4, shafi na 1981, lambar hadisi na 2556 [119]

Sahihu ibn huzaimah mujalladi na 3, shafi na 278, lambar hadisi na 2067, albani ya ingantashi [120]

Suratun nisa'I [121]

Sahihul buhari, mujalladi na 5, shafi na 2239 lambar hadisi na 5668 [122]

Sahihul buhari, mujalladi na 5, shafi na 2240 lambar hadisi na 5670 [123]

Sahihul buhari, mujalladi na 5, shafi na 2047 lambar hadisi na 5038 [124]

Abu nu'aim ne ya kawo shi cikin alhilyatu [125]

Mujalla ta na rayuwan muslunci a gobe al adad 146/ the debauchery of American womanhood 1424/6hijra [126]

Daga ikin littafin shuwagabannin turawa suna cewa: [127]

Suratul bakara ayata 120 [128]

Mujalla ta na rayuwan muslunci a gobe al adad 146/ the debauchery of American womanhood 1424/6hijra[129]

Musnad na imamu ahmad, lambar hadisi na 22265, albani ya inganta shi [130]

Tarihin aure/ wester mark/ [131]

Mace cikin alkur'ani na Abbas Mahmud al aqqad [132]

Sahihu ibn hibban, lambar hadisi na 456 kuma albani ya ingantashi [133]

Tirmiz da ahmad ne suka rawaito shi kuma albani ya inganta shi [134]

Umdatut tafsir, Ahmad shakir ya inganta shi cikin mukaddamar san a tahkikin undatut tafsir [135]

Mujallar azhar mujalladi na takwas 291 [136]

Mu bama muwafaka ga littafin dai daita Karin aure da zulumci! Da cewa Karin aure abun kyama ne sai dai idan abun da ake tsoro ya samu watan rashin adalci tsakanin mta [137]

Suratul bakara ayata 282 [138]

Suratun nur ayata 6-9 [139]

Suratun nisa'I ayata 34 [140]

Mace jikin alqur'ani na Mahmud al'aqqad [141]

Man th unknown p.93 [142]

Sahihul buhari, lambar hadisi na [143]

Suratun nisa'I ayata 19 [144]

Suratun nisa'I ayata 7 [145]

Cikin zilalul qur'an shafi na 588 [146]

Suratun nisa'I ayata 11 [147]

Sahihul buhari, lambar hadisi na 1233 [148]

Sahihul buhari, lambar hadisi na 853 [149]

Sunan ibn majjah hadisi na 2363, hadisi ne ingantacce [150]

Aikin mace cikin mizani na dakta Abdullahi dan wakil alsheikh [151]

Amincin duniya da musulunci shafi na 56 [152]

Duba cikin littafin alhijab wal sufur na Mustapha algalayini shafi na 94-95 [153]

Suratun nisa'I ayata 128 [154]

Sahihu ibn hibban lambar hadisi na 4075 kuma albani ya inganta shi [155]

Sahihul buhari, lambar hadisi na 6546 [156]

Sahihul buhari, lambar hadisi na 4843 [157]

Mustadrak ala sahihain lambar hadisi na 2695, kuma albani ya inganta shi [158]

Sahihul buhari, lambar hadisi na 1763 [159]

Sahihul buhari [160]

Suratu daha ayata 123 [161]

Suratun nisa'I ayata 1[162]

Suratul hujurat ayata 13 [163]

Suratul tauba ayata 81 [164]

Suratu al'imran ayata 195 [165]

Wata me bincike yar kasar italiya na wannan zamani wanda ta canza zuwa ga karantar tarihin musulunci na yanzu dana baya [166]